Jami’an Tsaron A Nan Iran Sun Kama Yan Kungiyar ISIS Kafin Su Aiwatar Da Hare-Hare
Published: 4th, June 2025 GMT
Jami’an Yansanda masu kula da ayyukan ta’addanci da kuma hana aukuwarsu a nan Iran sun sami nasarar kama wasu yan kungiyar ISIS 13 a duk fadin kasar daga ciki har da shugabansu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Brigadier General Saeed Montazer al-Mahdi kakakin rundunar FARAJA mai kula da fada da yan ta’adda yana fadar haka.
Labarin ya kara da cewa an kama yan ta’addan na ISIS a biranen Tehran, Qum, Esfahan da kuma Albus. Kuma an kama tare da su kayakin aiki wadanda suka hada da damarar boma bomai na kunan bakin waje da kuma jakunan da ake ratayawa a baya cike da abubuwan Facewa. Kakakin rundunar FARAJA y ace suna dauke da karin bayani nan gaba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Jami’in Gwamnatin Biden Na Amurka Ya Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Tafka Laifukan Yaki
Daya daga cikin manyan-manyan jami’an gwamnatin tsohon shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya bayyana cewa: “Babu tantama gwamnatin HK Isra’ila ta tafka laifukan yaki a kan Falasdinawa a zirin Gaza da ta killace.
Matthew Miller wanda ya yi aiki a matsayin kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka tun daga 2023 har zuwa karshen gwamnatin Joe Biden, ya fada wa tashar talabijin ta Sky News kan cewa; Isra’ilan ta tafka laifukan yaki.
Da aka yi masa tambaya a kan yakin Gaza a fadar White House, Miller ya ce; An yi ta samun tsabani dangane da yakin, sabani manya-manya wani lokacin kuma kananan sabani, kan yadda za a kare dangantakar Amurka da HK Isra’ila duk tare da abinda take aikatawa.”. Amma Miller ya tabbatar da cewa HK Isra’ilan ta tafka laifukan yaki wanda babu shakka a cikin hakan..
Da aka tambaye shi a kan, ko me ya sa a lokacin suke Mulki bai bayyana cewa HK Isra’ila tana aikata laufkan yaki ba? Sai ya amsa da cewa:
“Idan mutum yana cikin gwamnati, ba ya bayyana ra’ayinsa na kashin kansa, yana bayyana ra’ayin gwamnatin Amurka ne.”
Haka nan kuma ya ce; Aikin mai magana da yawun gwamnati, ko dai ka zama mai Magana da yawun shugaban kasa, ko gwmanatin kasar, amma idan baka cikin gwamnati, to za ka iya fadar ra’ayinka.”