Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah
Published: 3rd, June 2025 GMT
Wata hajiyar Najeriya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makkah na ƙasar Saudiyya.
Hajiya Jamila Muhammad ta rasu ne a yayin da alhazai ke shirin fara gudanar da aikin Hajji gadan-gadan.
Sakataren Hukumar Kin Dadin Alhazai ta Jirage Filato, Daiyabu Dauda, ya sanar a ranar Litinin cewa Hajiya Jamila ta rasu ne a asibitin Sarki Abdulaziz da ke Makkah, sakamakon tashin cutar suga.
Ya ce Amirul Hajj na jihar da wasu manyan jami’ai sun halarci jana’izar marigayiyar, kamar yadda Musulunci ta tanada.
Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga MakkaDa rayuwarta, yawan alhazan Najeriya da suka rasu a aikin Hajjin bana ya ƙaru zuwa mutum uku.
Kafin ita, Najeriya ta rsa alhazai biyu da suka hada da Hajiya Adizatu Dazumi daga Jihar Edo da kuma Alhaji Saleh Saleh daga Jihar Abiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Saudiyya ta rasu
এছাড়াও পড়ুন:
Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
An garzaya da ita asibiti, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta.
’Yansanda sun kama Bosede kuma suna bincike a kan lamarin.
Kakakin rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce za su tabbatar da adalci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp