Aminiya:
2025-06-05@04:10:19 GMT

Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah

Published: 3rd, June 2025 GMT

Wata hajiyar Najeriya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makkah na ƙasar Saudiyya.

Hajiya Jamila Muhammad ta rasu ne a yayin da alhazai ke shirin fara gudanar da aikin Hajji gadan-gadan.

Sakataren Hukumar Kin Dadin Alhazai ta Jirage Filato, Daiyabu Dauda, ya sanar a ranar Litinin cewa Hajiya Jamila ta rasu ne a asibitin Sarki Abdulaziz da ke Makkah, sakamakon tashin cutar suga.

Ya ce Amirul Hajj na jihar da wasu manyan jami’ai sun halarci jana’izar marigayiyar, kamar yadda Musulunci ta tanada.

Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga Makka

Da rayuwarta, yawan alhazan Najeriya da suka rasu a aikin Hajjin bana ya ƙaru zuwa mutum uku.

Kafin ita, Najeriya ta rsa alhazai biyu da suka hada da Hajiya Adizatu Dazumi daga Jihar Edo da kuma  Alhaji Saleh Saleh daga Jihar Abiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Saudiyya ta rasu

এছাড়াও পড়ুন:

Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga Makka

Jami’an Tsaron Saudiyya sun kori mutane sama da 205,000 da ke neman yin aikin Hajji ta barauniyar hanya daga birnin Makka a yayin da aikin Hajjin bana ya kawo jiki.

Daraktan Tsaron Jama’a kuma Shugaban Kwamitin Tsaron Hajji, Laftanar-Janar Mohammed Al-Bassami, ya bayyana cewa hukumomin kasar sun hana mutane sama da 269,000 marasa takardun izini shiga Makka, da kuma motoci 110,000 dauke da mahajjata ba bisa ka’ida ba da aka hana shiga.

An kuma kama 1,239 da suka yi yunkurin jigilar mahajjata ba bisa ka’ida ba, tare da ci tarar masu karya dokokin Hajji sama da 75,000, kuma tare da bankado ofisoshin aikin Hajji na bogi sama da 415.

Laftanar Janar Mohammed Al-Bassami ya sanar da hakan ne a ranar Lahadi, a yayin da yake jawabi game da yadda suka tsaurara matakan taro domin tabbatar da gudanar da aikin Hajjin bana cikin tsari da bin doka.

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta ba makarantu hutun kwana 10 Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne

Jami’in ya jaddada amfani da fasahar zamani don inganta tsare-tsaren tsaro, yana mai da nanata cewa jami’an tsaro suna sanya ido sosai kan duk wani mai karya doka, a kokarinsu na ganin an yin aikin hajjin bana cikin nasara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
  • Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda
  • Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Yi Tanadi Na Musamman Ga Alhazanta A Mina
  • Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga
  • Magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa
  • Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga Makka
  • NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa