Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah
Published: 3rd, June 2025 GMT
Wata hajiyar Najeriya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makkah na ƙasar Saudiyya.
Hajiya Jamila Muhammad ta rasu ne a yayin da alhazai ke shirin fara gudanar da aikin Hajji gadan-gadan.
Sakataren Hukumar Kin Dadin Alhazai ta Jirage Filato, Daiyabu Dauda, ya sanar a ranar Litinin cewa Hajiya Jamila ta rasu ne a asibitin Sarki Abdulaziz da ke Makkah, sakamakon tashin cutar suga.
Ya ce Amirul Hajj na jihar da wasu manyan jami’ai sun halarci jana’izar marigayiyar, kamar yadda Musulunci ta tanada.
Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga MakkaDa rayuwarta, yawan alhazan Najeriya da suka rasu a aikin Hajjin bana ya ƙaru zuwa mutum uku.
Kafin ita, Najeriya ta rsa alhazai biyu da suka hada da Hajiya Adizatu Dazumi daga Jihar Edo da kuma Alhaji Saleh Saleh daga Jihar Abiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Saudiyya ta rasu
এছাড়াও পড়ুন:
2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed
Datti Baba-Ahmed, wanda ya yi wa Peter Obi, takarar mataimaki a zaɓen 2023, ya ce yana goyon bayan Obi idan yana so ya sake yin takara a 2027, ko da ba tare da shi ba.
Peter Obi da Datti sun tsaya takara tare a 2023 sai dai sun ƙare a na uku.
NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule LamidoShugaba Bola Tinubu ne ya lashe zaɓen.
Datti, ya ce Obi yana da ’yancin sake tsayawa takara a ƙarƙashin LP.
Ya kuma ce ba dole ne sai Obi ya yi haɗin gwiwa da shi ba.
“Peter Obi mutum ne da nake girmamawa ƙwarai. Yana da damar sake fitowa takara a 2027, ko da ba tare da ni ba,” in ji Datti a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels.
Datti, wa ds tsohon Sanata ne, ya ce Najeriya na buƙatar shugabanni masu gaskiya da za su iya kawo ci gaba, ba masu alƙawuran ƙarya ba.
“Muna cikin wani yanayi mai muhimmanci. ’Yan Najeriya na buƙatar aiki ba uzuri ba. Muna buƙatar shugabanni masu cika alƙawari da gyara ƙasa,” in ji shi.
Game da shigar Peter Obi a wata haɗakar siyasa a jam’iyyar ADC, Datti ya ce hakan ba laifi ba ne.
“Haɗin gwiwa a siyasa ba cin amanar jam’iyya ba ne. Hakan al’ada ce a siyasa, inda mutane da jam’iyyu ke haɗuwa don cimma buri ɗaya.
“Ni ma na halarci wasu daga cikin tarukan. Ba wani abu ba ne da ya saɓa wa doka ko tsarin jam’iyya,” in ji shi.
Ya ce wannan haɗin gwiwar na da nufin samar wa ’yan Najeriya zaɓi mai kyau duba da halin da ake ciki.
Game da batun karɓa-karɓar mulki tsakanin Arewa da Kudu, Datti, ya ce kamata ya yi shugabancin ƙasa ya koma Kudu a 2027.
Ya ce wannan ba lissafin siyasa ba ne, amma manufar adalci da haɗin kai a ƙasa mai yawan ƙabilu kamar Najeriya ne.