Aminiya:
2025-06-05@00:42:55 GMT

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa

Published: 3rd, June 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na ci gaba da raba dubban mutane da matsugunansu, tare da lalata dukiyoyi a faɗin Najeriya.

Ko a makon da ya gabata, wasu al’ummomi a Karamar Hukumar Mokwa da ke Jihar Neja sun fuskanci irin wannan ambaliya da ta yi sanadiyyar rasa ɗaruruwan rayuka da dukiyoyi masu yawa.

NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa DAGA LARABA: “Sai Na Tara Kudin Cin Abinci Na Nake Iya Siyan Audugar Al’ada”

Ko waɗanne hanyoyi za a bi domin kauce wa ɓarnar ambaliya a Najeriya?

Wannan ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa kaucewa ambaliyar ruwa Mokwa

এছাড়াও পড়ুন:

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna

ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu a Karamar Hukumar Kaduna Sout

Shirin Dawo da Yara Makaranta na Gwamnatin Jihar Kaduna Mai suna ROOSC ya kaddamar da rabon kayan koyon karatu ga dalibai a Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu, Jihar Kaduna.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a Makarantar Firamare ta LEA da ke Unguwar Mu’azu, inda manyan masu ruwa da tsaki kan harkar ilimi, musamman shugabannin addini da na al’umma, suka halarta.

Da yake jawabi a wajen taron, Ko’odinetan ROOSC a Jihar Kaduna, Mr. Ezra Angai, ya bayyana cewa wannan shiri hadin gwiwa ne tsakanin Gwamnatin Jihar Kaduna da abokan ci gaba da kuma kungiyoyin aiwatar da shirin, domin inganta samun ilimi mai nagarta ga yaran da ba sa zuwa makaranta.

Ya bayyana cewa, ana aiwatar da shirin ne karkashin kulawar Ma’aikatar Ilimi ta jihar tare da hadin gwiwar kungiyoyin Save the Children da UNICEF.

“An samu kudade daga bashin sauki da tallafin da Bankin Raya Kasashen Musulmi (Islamic Development Bank) ya bayar domin aiwatar da wannan shiri,” in ji shi.

Mr. Angai ya ce, Gwamnatin Jihar Kaduna ta samu bashin sauki da tallafi domin magance matsalar yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin jihar.

Ya kara da cewa, shirin zai gina sabbin makarantu guda 102 tare da gyara wasu 170 da ke aiki a yanzu, inda ake sa ran samun kimanin yara 200,000 da ba sa zuwa makaranta a kan gaba a cikin shekara hudu a fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

Shi ma da yake jawabi, Jagoran Save the Children a jihar, Malam Tanko Mohammed Langaya, ya bayyana cewa shirin ROOSC yana da kudurin raba kayan koyon karatu da koyarwa sama da 500,000 ga dalibai a makarantu a matsayin wani muhimmin bangare na aiwatar da shirin.

“Wadannan kayan karatu ba wai na kari ba ne kawai, su ne tushen ilimi mai nagarta. Tabbatar da cewa kowane yaro yana da kayan karatu masu dacewa da shekarunsa da al’adarsa da kuma masu jan hankali, muhimmin mataki ne wajen samar da ingantaccen daidaito da ilimi ga kowa da kowa a Jihar Kaduna.”

Ko’odinetan shirin daga Save the Children, Mr. Emmanuel Mbursa, ya jaddada muhimmancin raba kayan karatu guda 100,000, yana mai cewa hakan babbar nasara ce a kokarin dawo da yaran da suka daina zuwa makaranta cikin tsarin ilimin gargajiya.

Ya kuma bayyana bukatar samun goyon bayan al’umma domin dorewar shirin.

A nasa jawabin, Daraktan Tsare-tsare a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Mista Salisu Bala, ya ce shirin na ROOSC yana da nufin bai wa yara ‘yan shekaru 6 zuwa 11 da matasa ‘yan shekaru 12 zuwa 18 da ke wajen makaranta damar samun ilimin firamare mai inganci.

Tun da farko, Shugaban Kwamitin Gudanar da Makarantun Firamare SBMC na Kaduna South, Alhaji Usman Sani, wanda kuma shi ne Hakimin Badikko, ya jaddada rawar da ilimi ke takawa wajen magance matsalolin rashin tsaro da matsin tattalin arziki a kasar.

Ya bukaci iyaye da shugabannin al’umma da su tabbatar cewa dukkan yara masu shekaru na zuwa makaranta suna halartar makaranta, yana mai bayyana damuwa kan rashin isasshen samun ilimin yara kanana a wasu yankunan jihar.

Alhaji Usman Sani ya yabawa Gwamna Uba Sani bisa kudurinsa na samar da ilimi ga kowa da kowa, yana mai cewa shirin ROOSC wata babbar hanya ce ta tabbatar da ingantacciyar makoma ga yaran Jihar Kaduna.

A halin yanzu, kananan hukumomi tara aka riga aka zaba domin rabon kayan koyon karatu. Sun hada da: Kaduna South, Igabi, Kaduna North, Sabon Gari, Soba da Lere.

Sauran sune: Kachia da Jema’a da kuma Kauru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji
  • Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano
  • ROOSC Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Koyon Karatu A Kaduna
  • Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
  • Nasarorin Shekaru Biyun Tinubu Shaida Ne Ta Shugaba Mai Hangen Nesa – Ministan Yada Labarai
  • Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700
  • Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
  • Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah
  • NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa