Rundunar ‘yansanda a jihar Gombe ta umurci rufe duk wata tashar sauka ko daukar fasinjoji a cikin garin Gombe ciki har da fitacciyar tashar Dadin Kowa, inda ta ce, tashar Ibrahim Hassan Dan-Kwambo ce kadai halastacciya.

 

Bugu da kari, motocin haya da ke dauke da amintaccen launin kala na gwamnati a cikin garin Gombe ne kadai suke da izinin zirga-zirgar daukar fasinjoji a birnin.

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Wannan umarni na kunshe ne acikin wata sanarwar manema labarai da jami’in hulda da jama’a na rundunar a jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, a ranar Litinin, 2 ga watan Yunin 2025.

“An dauki wannan matakin ne daidai da kudurin gwamnati na maido da bin doka, inganta tsaro, da kuma tabbatar da lafiyar fasinjoji. An umurci dukkan masu sana’ar tuki na kasuwanci da su gudanar da dukkan ayyukan lodi da sauke kaya a tashar motoci ta Ibrahim Hassan Dan-kwambo kadai da ke babban birnin jihar.

 

“Duk wani wanda aka samu ya taka doka zai fuskanci tsauraran sakamako na shari’a, gami da kamawa, gurfanar da shi, da yuwuwar kama motarsa.” In Ji DSP Abdullahi

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga Makka

Jami’an Tsaron Saudiyya sun kori mutane sama da 205,000 da ke neman yin aikin Hajji ta barauniyar hanya daga birnin Makka a yayin da aikin Hajjin bana ya kawo jiki.

Daraktan Tsaron Jama’a kuma Shugaban Kwamitin Tsaron Hajji, Laftanar-Janar Mohammed Al-Bassami, ya bayyana cewa hukumomin kasar sun hana mutane sama da 269,000 marasa takardun izini shiga Makka, da kuma motoci 110,000 dauke da mahajjata ba bisa ka’ida ba da aka hana shiga.

An kuma kama 1,239 da suka yi yunkurin jigilar mahajjata ba bisa ka’ida ba, tare da ci tarar masu karya dokokin Hajji sama da 75,000, kuma tare da bankado ofisoshin aikin Hajji na bogi sama da 415.

Laftanar Janar Mohammed Al-Bassami ya sanar da hakan ne a ranar Lahadi, a yayin da yake jawabi game da yadda suka tsaurara matakan taro domin tabbatar da gudanar da aikin Hajjin bana cikin tsari da bin doka.

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta ba makarantu hutun kwana 10 Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne

Jami’in ya jaddada amfani da fasahar zamani don inganta tsare-tsaren tsaro, yana mai da nanata cewa jami’an tsaro suna sanya ido sosai kan duk wani mai karya doka, a kokarinsu na ganin an yin aikin hajjin bana cikin nasara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah
  • ‘Yansanda A Kano Sun Gargadi Sarki Sanusi Kan Yekuwar Fitowa Hawan Sallah
  • Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga Makka
  • Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno
  • Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin
  • Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka
  • Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno