A wani yunkuri na rage adadin yara da suka daina zuwa makaranta, Gwamnatin Jihar Kaduna ta kaddamar da shiri mayarda yara 200,000 zuwa makaranta a cikin shekaru hudu masu zuwa, karkashin shirin Reaching Out-of-School Children (ROOSC).

 

An bayyana wannan shiri ne a wani taron bita na kwanaki biyu da aka shirya tare da haɗin gwiwar Save the Children.

 

A cewar, wakilin Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Salisu Baba Lawal shirin zai shafi dukkan ƙananan hukumomi 23 a faɗin jihar.

 

“Wannan shiri na Gwamnatin Jihar Kaduna ne tare da haɗin gwiwar abokan ci gaba da masu aiwatar da ayyuka,” in ji shi.

 

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta samo lamunin tallafin kudi domin aiwatar da wannan shiri da nufin maganin matsalar yara da suka bar makaranta a faɗin jihar,” ya ƙara da cewa.

 

“Zuwo yanzu, an riga an horar da malamai 405, an gina sabbin makarantu 102, sannan ana ci gaba da gyara wasu makarantu 170.

 

Shirin yana ƙarfafa rajistar yara a makaranta da inganta koyarwa da samar da ingantaccen yanayi na koyo da koyarwa.”

 

Save the Children International da UNICEF su ne manyan abokan hulɗar wannan shiri, kuma yana samun goyon bayan kai tsaye daga Gwamna Uba Sani.

 

Save the Children ta raba kayan aiki da horar da malamai a karkashin shirin Reaching Out-of-School Children na Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Ma’aikatar Ilimi.

 

Shirin ROOSC yana mai da hankali kan ɗorewa, daidaito tsakanin jinsi, da kuma tallafawa marasa galihu, domin tabbatar da damar samun ingantacciyar ilimin firamare ga yara, matasa, da samari a fadin Jihar Kaduna.

 

Save the Children da UNICEF sun samu wakilci daga gwamnatin jihar ta hannun Ma’aikatar Ilimi don inganta tsarin koyarwa (Save the Children) da kuma ƙarfafa tsarin ilimi gaba ɗaya (UNICEF).

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin Makaranta Mayarda yara Zuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Kirikasamma

Kwamatin kananan hukumomi na Majalisar Dokokin jihar Jigawa ya duba ayyukan raya kasa da karamar hukumar Kirikasamma ta samu nasarar gudanarwa daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu.

Shugaban Kwamatin, Alhaji Aminu Zakari, ya kafa kananan kwamitoci guda biyu domin samun nasarar tantance ayyukan a cikin garin   Kirikasamma da kauyuka.

Karamin Kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar
Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashimu Kanya, ya duba aikin sanya soma da tona riniyar tuka tuka a mayanka da magudanin ruwa a garin Marma da aikin gina rumfunan kasuwa a garuruwan Tasheguwa, Marma, Dilmari da Madaci.

Alhaji Ibrahim Hashim Kanya ya bayyana wa shugaban kamsilolin karamar hukumar wanda ke yiwa tawagar rakiya, Malam Isyaku Abdullahi, muhimmancin ziyarar duba ayyukan Gwamnati dan tabbatar da inganci.

Sai Kuma karamin Kwamati na biyu bisa jagorancin wakilin mazabar Kiyawa Alhaji Yahaya Muhammad Andaza wanda ya duba aikin gyaran hanyar Gafta zuwa Baturiya akan fiye da naira milyan 4 da dubu dari 2, wadda ambaliyar ruwa ta lalata a daminar bara da kuma aikin gina rumfar kasuwa a garin Baturiya.

Tun da farko a sakatariyar karamar hukumar Kirikasamma, Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa Kuma wakilin mazabar Gwiwa,
Alhaji Aminu Zakari ya ce ziyarar Kwamatin na daga nauyin da tsarin mulki ya dorawa bangaren majalisa wajen duba manufofi da shiryeyen Gwamnati baya da yin doka da amincewa da kasafin kudin kowacce shekara.

Alhaji Aminu Zakari ya ce Kwamatin Yana duba kundin bayanan harkokin Kudi da na sha’anin Mulki da su ka hadar da littafin shiga da fitar kudade da takardun biyan kudade na voucher da alkaluman tattara kudaden shiga da kundin tarukan kwamitocin karamar hukuma domin tabbatar da kashe kudaden Gwamnati ta hanyar da ta dace domin wanzuwar shugabanci nagari.

A cewar sa, daga yanzu Daraktan tsare-tsare ya zamo daga cikin masu rattaba hannu kan takardun kashe kudade, mataimakin shugaban karamar hukumar zai rike sashen kula da ruwa da tsafta a matsayin Kansila maras gafaka.

Yayi nuni da cewar, akwai bukatar karamar hukumar ta gina ajujuwa guda 2 na makarantun ‘ya’Yan fulani makiyaya domin shigo da su cikin tsare tsaren ci gaban al’umma.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Kirikasamma, Alhaji Muhammad Maji Wakili Marma, ya lura da gudummawar da bangaren majalisa ke bayarwa wajen gudanar da harkokin Gwamnati a matakin jiha da kananan hukumomi.

Alhaji Maji Wakili ya bada tabbacin aiki da shawarwari Kwamatin domin karfafa matarka cigaban karamar hukumar.

Sauran Yan Kwamatin sun hadar da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da sakataren Kwamatin Kuma Akawun Majalisa Alhaji Yusha’u Muhammad, da oditoci biyu da mataimakan sakatare.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati
  • DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Kirikasamma
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar