A wani yunkuri na rage adadin yara da suka daina zuwa makaranta, Gwamnatin Jihar Kaduna ta kaddamar da shiri mayarda yara 200,000 zuwa makaranta a cikin shekaru hudu masu zuwa, karkashin shirin Reaching Out-of-School Children (ROOSC).

 

An bayyana wannan shiri ne a wani taron bita na kwanaki biyu da aka shirya tare da haɗin gwiwar Save the Children.

 

A cewar, wakilin Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Salisu Baba Lawal shirin zai shafi dukkan ƙananan hukumomi 23 a faɗin jihar.

 

“Wannan shiri na Gwamnatin Jihar Kaduna ne tare da haɗin gwiwar abokan ci gaba da masu aiwatar da ayyuka,” in ji shi.

 

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta samo lamunin tallafin kudi domin aiwatar da wannan shiri da nufin maganin matsalar yara da suka bar makaranta a faɗin jihar,” ya ƙara da cewa.

 

“Zuwo yanzu, an riga an horar da malamai 405, an gina sabbin makarantu 102, sannan ana ci gaba da gyara wasu makarantu 170.

 

Shirin yana ƙarfafa rajistar yara a makaranta da inganta koyarwa da samar da ingantaccen yanayi na koyo da koyarwa.”

 

Save the Children International da UNICEF su ne manyan abokan hulɗar wannan shiri, kuma yana samun goyon bayan kai tsaye daga Gwamna Uba Sani.

 

Save the Children ta raba kayan aiki da horar da malamai a karkashin shirin Reaching Out-of-School Children na Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Ma’aikatar Ilimi.

 

Shirin ROOSC yana mai da hankali kan ɗorewa, daidaito tsakanin jinsi, da kuma tallafawa marasa galihu, domin tabbatar da damar samun ingantacciyar ilimin firamare ga yara, matasa, da samari a fadin Jihar Kaduna.

 

Save the Children da UNICEF sun samu wakilci daga gwamnatin jihar ta hannun Ma’aikatar Ilimi don inganta tsarin koyarwa (Save the Children) da kuma ƙarfafa tsarin ilimi gaba ɗaya (UNICEF).

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin Makaranta Mayarda yara Zuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara

Aƙalla mutane 20 ne suka mutu bayan wani hari da jiragen sama na sojojin Najeriya (NAF) ya kai domin fatattakar ’yan bindiga a a Jihar Zamfara.

Jiragen sojin sun kashe wasu ’yan sa-kai bisa kuskure, a yayin da ’yan sa-kan suke ƙoƙarin fatattakar ’yan bindiga da suka kai hari a yankin Mani a Ƙaramar Hukumar Maru.

Jiragen sojin sun kai hare-haren ne domin fatattakar ’yan bindiga da suka kai wa manoma hari a kan babura da rana tsaka.

Mazauna yankin sun ce bayan ’yan bindiga sun sace manoma sama da 50 ne jirgin sojin ya amsa kiran gaggawa, amma aka samu kuskure ya kashe wasu ’yan sa-kai da ke ƙoƙarin fatattakar maharan.

Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa

Wani mazaunin yankin ya shaida wa kafar BBC cewa, “Mun sanar da jami’an tsaro bayan harin, amma kawai sai muka ga jirgin ya zo ya kashe ’yan sa-kai na mu.”

Wani mazaunin garin ya ce, a yayin da jama’a ke ƙoƙarin taimaka wa wadanda aka kai wa hari, sai ga wani jirgin saman soji ya iso.

Ya ce, “’Yan bindigar sun tafi da mutane 50, amma yayin da muke ƙoƙarin kai ɗauki, sai muka ga jirgin soji, kuma ya fara harbin mu. Kowa ya gudu neman mafaka,” inda ya ƙara da cewa sun yi kamar matattu ne don su tsira.

Wani mazaunin kuma ya yi kira ga jami’an tsaro da su ƙara yawa, inda ya buƙaci a yankin amma su yi taka-tsantsan yayin gudanar da ayyukan.

Har yanzu sojojin Najeriya ba su ce komai ba game da lamarin.

Idan ba a manta ba, ire-iren wannan harin huskure ya faru a baya a yankin Jihar Zamfara. A watan Janairun 2025, wani harin jirgin saman sojin Najeriya ya kashe mutane 16 bisa kuskure, ciki har da ’yan sa-kai da manoma, a ƙauyen Tungar Kara a Jihar Zamfara, bayan an zaci su ’yan bindiga ne.

Hakazalika, a watan Disambar 2024, wani harin jirgin sama a Jihar Sakkwato ya kashe fararen hula 10 a sakamakon abin da Gwamnan jihar ya bayyana a matsayin harin kuskure kan fararen hula.

A watan Disamban shekarar 2023 wani jirgin soja ya kai irin harin inda ya kashe sama da fararen hula kimanin 100 a wurin taron Mauludi a yankin Tudun Biri da ke Ƙaramar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
  • Gwamnn Zamfara Ya Ba Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Barka Da Sallah
  • Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah
  • Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta Da Kashi 2,200%
  • Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a Zamfara
  • Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara
  • Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
  • ECOWAS Da CORET Sun Shirya Taro Domin Cigaban Makarantun Fulani A Kaduna