Aminiya:
2025-09-18@02:19:22 GMT

Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba

Published: 20th, May 2025 GMT

Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Jihar Kano, ta sanar da dakatar da duk wani nau’in tallan magungunan gargajiya a cikin fina-finai, a kan titi ko amfani da lasifika.

Wannan na cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, wadda Jami’in Yaɗa Labaran Hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya raba wa manema labarai.

’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a Abuja

Shugaban hukumar ya ce wannan matakin na da nufin kare martabar masana’antar fina-finai da kuma tabbatar da cewa duk wani bayani da ke zuwa ga jama’a ya bi ƙa’idoji da doka.

“Yawancin tallace-tallacen maganin gargajiya da ake yi a tituna ko kuma a cikin fina-finai suna karya dokokin da hukumarmu ta gindaya.

“Wannan dalili ne ya sa muka ɗauki matakin dakatar da duk wata hanya da ake amfani da ita wajen wannan talla, har sai mun tantance su tare da bayar da sahalewa,” in ji El-Mustapha.

Hukumar ta bayyana cewa daga ranar Laraba, 21 ga watan Mayu, 2025, duk masu ruwa da tsaki a harkar maganin gargajiya dole ne su miƙa tsarin tallace-tallacensu domin tantancewa cikin mako guda, ko kuma su fuskanci hukuncin hukumar.

“Mun bai wa kowa kwana bakwai ya gabatar da tsarin tallarsa domin mu duba.

“Wannan ya shafi masu fina-finai da kuma waɗanda ke yawo da lasifika a titi. Doka za ta ɗauki mataki a kan duk wanda ya saɓa,” cewar El-Mustapha.

A cikin wannan sanarwar, shugaban hukumar ya kuma buƙaci haɗin gwiwar tashoshin talabijin da Hukumar Kula da Kafafen Yaɗa Labarai ta Ƙasa (NBC), domin ganin an daƙile abin da ka iya shafar tarbiyya da lafiyar al’umma.

“Muna kira ga tashoshin talabijin da hukumar NBC su mara mana baya wajen tabbatar da bin doka da oda a fannin yaɗa bayanai, musamman masu nasaba da magunguna da lafiya. Wannan zai taimaka wajen kare martabar fina-finai da kuma lafiyar al’umma,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatarwa kannywood Magungunan Gargajiya Tantancewa

এছাড়াও পড়ুন:

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

A ƙalla fasinjoji 17 ne suka rasa rayukansu bayan wata motar haya ta faɗa cikin wata gada da ta ruguje a kan titin Gwalli da ke ƙaramar hukumar Gummi, jihar Zamfara.

A cewar hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa (FRSC) reshen Zamfara, hatsarin ya faru ne a daren Lahadi lokacin da motar ɗauke da kaya da fasinjoji ta faɗa cikin gadar da ta ruguje. Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, SRC Isah Aliyu, ya tabbatar da lamarin a wata sanarwa da ya fitar.

Kwamandan FRSC na jihar, CC Aliyu Magaji, wanda ya ziyarci wurin hatsarin, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa da asarar rayukan, inda mafi yawansu mata ne. Ya ce hatsarin ya biyo bayan nauyin da aka ɗora wa motar fiye da ƙima da kuma tafiya da daddare.

Hukumar ta gode wa mazauna yankin da suka gaggauta taimakawa wajen ceto wasu daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su. Kwamanda Aliyu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin Zamfara da al’ummar Gummi, tare da yin kira ga direbobi su rika bin ƙa’idojin hanya da kuma guje wa tuƙa mota da dare domin kare rayuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara