Aminiya:
2025-06-14@14:12:55 GMT

Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba

Published: 20th, May 2025 GMT

Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Jihar Kano, ta sanar da dakatar da duk wani nau’in tallan magungunan gargajiya a cikin fina-finai, a kan titi ko amfani da lasifika.

Wannan na cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, wadda Jami’in Yaɗa Labaran Hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya raba wa manema labarai.

’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a Abuja

Shugaban hukumar ya ce wannan matakin na da nufin kare martabar masana’antar fina-finai da kuma tabbatar da cewa duk wani bayani da ke zuwa ga jama’a ya bi ƙa’idoji da doka.

“Yawancin tallace-tallacen maganin gargajiya da ake yi a tituna ko kuma a cikin fina-finai suna karya dokokin da hukumarmu ta gindaya.

“Wannan dalili ne ya sa muka ɗauki matakin dakatar da duk wata hanya da ake amfani da ita wajen wannan talla, har sai mun tantance su tare da bayar da sahalewa,” in ji El-Mustapha.

Hukumar ta bayyana cewa daga ranar Laraba, 21 ga watan Mayu, 2025, duk masu ruwa da tsaki a harkar maganin gargajiya dole ne su miƙa tsarin tallace-tallacensu domin tantancewa cikin mako guda, ko kuma su fuskanci hukuncin hukumar.

“Mun bai wa kowa kwana bakwai ya gabatar da tsarin tallarsa domin mu duba.

“Wannan ya shafi masu fina-finai da kuma waɗanda ke yawo da lasifika a titi. Doka za ta ɗauki mataki a kan duk wanda ya saɓa,” cewar El-Mustapha.

A cikin wannan sanarwar, shugaban hukumar ya kuma buƙaci haɗin gwiwar tashoshin talabijin da Hukumar Kula da Kafafen Yaɗa Labarai ta Ƙasa (NBC), domin ganin an daƙile abin da ka iya shafar tarbiyya da lafiyar al’umma.

“Muna kira ga tashoshin talabijin da hukumar NBC su mara mana baya wajen tabbatar da bin doka da oda a fannin yaɗa bayanai, musamman masu nasaba da magunguna da lafiya. Wannan zai taimaka wajen kare martabar fina-finai da kuma lafiyar al’umma,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatarwa kannywood Magungunan Gargajiya Tantancewa

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran

Isra’ila ta kaddamar da hare hare kan wasu gine-gine da cibiyoyi a sassa daban daban na Iran ciki har da Tehran babban birni a cikin daren jiya wayewar wannan safiya ta Juma’a.

Kafofin yada labarai na Iran sun ce akwai mata da yara da dama daga cikin wadanda suka yi shahada a hare-haren.

An kuma bayar da rahoton kai hari a wurare a Natanz, Khorramabad, da Khondab, da dai sauransu.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin da Isra’ila ta kai wa Iran zai kai tsawon kwanaki idab akwai bukatar hakan.

“Za a ci gaba da gudanar da wannan aiki na tsawon kwanaki kamar yadda ake tsara don kawar da wannan barazanar,” in ji Netanyahu a cikin wata sanarwa ta bidiyo.

Hare-haren da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai kan Tehran ya yi sanadiyar shahadar wasu fitattun masana kimiyyar nukiliya na Iran, Mohammad Mahdi Tehranchi da Fereydoon Abbasi, dama wasu fararen hula.

Tehranchi shi ne shugaban jami’ar Azad ta Musulunci ta Iran.

Fereydoon Abbasi ya kasance tsohon shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran.

An dakatar da zirga-zirgar jiragai a filin jirgin saman Imam Khumaini na Tehran.

Harin ya zo ne kwanaki biyu gabanin wani sabon zagaye na shawarwarin nukiliyar Iran da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Iran Ta Ce: Rashin Dakatar Da Uranium Da Dage Takunkumi Sune Hanyar Warware Takaddamar Da Ita
  • An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Sake Tunzura Iran Shirin Makamashin Nukiliyarta Zai Fuskanci Martani