Yaƙi ya ɓarke tsakanin Indiya da Pakistan
Published: 7th, May 2025 GMT
Yaƙi ya ɓarke tsakanin Indiya da Pakistan yayin da a safiyar wannan Larabar ƙasashen biyu suka riƙa yi wa juna musayar wuta da manyan makaman atilari.
Hakan na zuwa ne bayan harin da Indiya ƙaddamar kan Islamabad da sassafe, lamarin da ke nuna ɓarkewar rikici tsakanin maƙwaftan biyu masu makaman nukiliya.
Indiya ta ce ta ƙaddamar da jerin hare-hare ta sama a kan wurare cikin Pakistan, a matsayin ramuwar-gayya ta harin da wasu ’yan bindiga suka kai yankin Kashmir da ke ƙarƙashin ikonta a watan da ya gabata — wanda a lokacin aka kashe fararen hula 26.
Kafafen yaɗa labarai na Pakistan sun bayar da rahoton jerin fashe-fashe a wurare daban-daban ciki har da birnin Muzaffarabad, da har wutar lantarki ta ɗauke.
Mutane sun mutu a dukkan ɓangarorin, saboda a yayin da Pakistan ta ce harin Indiya ya yi sanadin mutuwar mutane aƙalla takwas, a nata ɓangaren, Indiya ta ce fararen hula 3 sun mutu a kusa da Kashmir sakamakon harba manyan makaman atilari da Pakistan ta yi.
Wani jami’in gwamnatin Indiya, Azhar Majid ya ce Indiyawa 8 ne suka mutu, kana 29 suka samu rauni a wannan Laraba a garin Poonch na Kashmir, kusa da iyaka da Pakistan.
Ministan Tsaron Pakistan Khawaja Asif ya ce an harbo jiragen yaƙin India biyar kuma an yi garkuwa da sojojin India takwas a matsayin fursunonin yaƙi.
Tun da farko, Ministan Watsa Labaran Pakistan Attaullah Tarar ya shaida wa TRT cewa an harbo jirgi guda ɗaya a birnin Akhnoor da ke yankin Kashmir wanda ake taƙaddama a kansa.
Sannan aka harbo wani jirgin a birnin Ambala na ƙasar Indiya, kazalika an harbo jirgi marasa matuƙi a lardin Jammu na ɓangaren Kashmir da ke ƙarƙashin ikon Indiya.
Tarar ya ƙara da cewa sojojin Pakistan sun mayar da martani ne kan harin da India ta kai ƙasar da makamai masu linzami waɗanda ta harba a yankunan “fararen-hula.”
Wani mai magana da yawun rundunar sojojin Pakistan ya ce sun “lalata” wasu kayayyakin tsaron India.
Indiya da Pakista sun sha gwabza faɗa tun bayan kafa su a shekarar 1947 da Turawan Birtaniya suka yi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Indiya
এছাড়াও পড়ুন:
Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
Trump ya ce hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, lallai zai kara rura wutar rikici a ci gaba da yakin da ake yi tsakanin Iran da Isra’ila.
Sai dai ministan harkokin wajen Iran Seyed Abbas Araghchi ya yi Allah wadai da harin da Amurka ta kai da cewa “abin takaici ne” sannan ya ce Iran ta tanadi “dukkan zabin kare ‘yancinta”, yana mai jaddada cewa Amurka za ta fuskanci “tsauraran sakamako”.
Araghchi ya kara da cewa, Amurka ta keta kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya a matsayinta na mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.
Bugu da kari, wani dan Majalisar kasar Iran, ya kara da cewa, “babu wani mummunan lahani a wuraren, kuma dama tun kafin harin, an riga an kwashe duk wasu abubuwa masu muhimmanci na tashoshin nukiliyar”.
Tun da farko, Tehran ta yi gargadin cewa za ta kai hari kan muradun Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya domin daukar fansa kan duk wani hari da Amurka ta kai, kuma ya zuwa yanzu ta harba makamai masu linzami kan Isra’ila, inda aka ji karar fashewar wasu abubuwa a birnin Kudus.
A halin da ake ciki, kawunan ‘yan majalisar dokokin Amurka ya rabu dangane da shigar kasar, inda ‘yan jam’iyyar Republican suka yabawa Trump, yayin da ‘yan jam’iyyar Democrat suka yi gargadin cewa an jefa Amurka cikin wani yakin da ba nata ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp