Yaƙi ya ɓarke tsakanin Indiya da Pakistan
Published: 7th, May 2025 GMT
Yaƙi ya ɓarke tsakanin Indiya da Pakistan yayin da a safiyar wannan Larabar ƙasashen biyu suka riƙa yi wa juna musayar wuta da manyan makaman atilari.
Hakan na zuwa ne bayan harin da Indiya ƙaddamar kan Islamabad da sassafe, lamarin da ke nuna ɓarkewar rikici tsakanin maƙwaftan biyu masu makaman nukiliya.
Indiya ta ce ta ƙaddamar da jerin hare-hare ta sama a kan wurare cikin Pakistan, a matsayin ramuwar-gayya ta harin da wasu ’yan bindiga suka kai yankin Kashmir da ke ƙarƙashin ikonta a watan da ya gabata — wanda a lokacin aka kashe fararen hula 26.
Kafafen yaɗa labarai na Pakistan sun bayar da rahoton jerin fashe-fashe a wurare daban-daban ciki har da birnin Muzaffarabad, da har wutar lantarki ta ɗauke.
Mutane sun mutu a dukkan ɓangarorin, saboda a yayin da Pakistan ta ce harin Indiya ya yi sanadin mutuwar mutane aƙalla takwas, a nata ɓangaren, Indiya ta ce fararen hula 3 sun mutu a kusa da Kashmir sakamakon harba manyan makaman atilari da Pakistan ta yi.
Wani jami’in gwamnatin Indiya, Azhar Majid ya ce Indiyawa 8 ne suka mutu, kana 29 suka samu rauni a wannan Laraba a garin Poonch na Kashmir, kusa da iyaka da Pakistan.
Ministan Tsaron Pakistan Khawaja Asif ya ce an harbo jiragen yaƙin India biyar kuma an yi garkuwa da sojojin India takwas a matsayin fursunonin yaƙi.
Tun da farko, Ministan Watsa Labaran Pakistan Attaullah Tarar ya shaida wa TRT cewa an harbo jirgi guda ɗaya a birnin Akhnoor da ke yankin Kashmir wanda ake taƙaddama a kansa.
Sannan aka harbo wani jirgin a birnin Ambala na ƙasar Indiya, kazalika an harbo jirgi marasa matuƙi a lardin Jammu na ɓangaren Kashmir da ke ƙarƙashin ikon Indiya.
Tarar ya ƙara da cewa sojojin Pakistan sun mayar da martani ne kan harin da India ta kai ƙasar da makamai masu linzami waɗanda ta harba a yankunan “fararen-hula.”
Wani mai magana da yawun rundunar sojojin Pakistan ya ce sun “lalata” wasu kayayyakin tsaron India.
Indiya da Pakista sun sha gwabza faɗa tun bayan kafa su a shekarar 1947 da Turawan Birtaniya suka yi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Indiya
এছাড়াও পড়ুন:
AU, ta yi tir da harin baya bayan nan a tashar ruwan Sudan
Kungiyar Tarayyar Afrika (AU), ta yi tir da hari na baya-bayan nan da aka kai Port Sudan, muhimmin birni a kasar Sudan dake cikin ’yan kalilan da yakin da ake yi a kasar bai shafa ba.
Port Sudan ya taka muhimmiyar rawa a matsayin cibiyar jigila da ayyukan agaji, yayin da ake ci gaba da gwabza fada a Sudan.
Kungiyar AU mai mambobi 55 ta yi gargadin cewa, kai hari birnin zai kawo tsaiko ga kokarin da ake yi na wanzar da zaman lafiya a kasar.
Rahotanni daga kafafen yada labarai na cewa, kungiyar RSF ta kai hari da jirgi mara matuki zuwa filin jirgin sama na sojoji, da sauran wuraren dake filin jirgin sama na kasa da kasa na Port Sudan, a ranar Lahadi.
An ce harin shi ne irinsa na farko da RSF din ta kai Port Sudan
Kafafen watsa labaran cikin gida sun ba da rahoton kai hari tashar jiragen ruwa da wasu gine-ginen gwamnati.
An ji tare da ganin fashewar bama-bamai da wuta nan da can a birnin na Port Sudan, wanda wannan shi ne kwana na uku a jere da birnin ke shan ruwan bama-bamai da ake kai harin ta hanyar kananan jiragen sama marassa matuka, kamar yadda wasu kafofin watsa labarai na kasar ke bayyanawa.
Su ma makwabtan kasar ta Sudan, Masar da Saudiyya sun yi Alllwadarai da hare haren , ita ma majaliasar dinkin duniya ta nuna damuwa a kai.
Tun watan Afirilu na 2023 Sudan ta fada wannan mummuna yakin basasa tsakanin kungiyar ta RSF da kuma rundunar sojin kasar wadanda a da suke tare – rikici kann sabanin mayar da mulki tsarin farar hula ya raba kansu.
Rikicin ya raba mutum ,iliyan 12 da muhallinsu kuma ya jefa rabin yawan alummar kasar cikin matsananciyar yunwa, kamar yadda majalaisar dinkin duniya ta ce.