HausaTv:
2025-05-04@14:34:42 GMT

An rantsar da Brice Nguema a matsayin shugaban Gabon

Published: 4th, May 2025 GMT

An rantsar da mista Brice Nguema a matsayin shugaban kasar Gabon, a birnin Libreville fadar mulkin kasar

Shugabannin kasashen Senegal, da Equatorial Guinea, da Rwanda, da dai sauransu na dag cikin bakin da suka halarci bikin.

An ce, bikin rantuwar kama aiki na wannan karo shi ne irinsa na farko a kasar Gabon mai bude kofa ga jama’ar kasar, don haka aka samu kimanin mutane 40,000 da suka je kallon bikin.

Kafin hakan an rantsar da Brice Nguema bayan ya lashe babban zaben kasar da ya gudana a shekarar nan ta 2025, inda ya yi nasarar lashe kaso 94.85% na jimillar kuri’un da aka kada.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Share Filin Noma Kadada 100 Don Karfafa Matasa Su Yi Noma A Babura Jihar Jigawa

Shugaban karamar hukumar Babura ta jihar Jigawa, Malam Hamisu Muhammad Garu, ya kaddamar da shirin karfafa aikin gona da nufin sanya matasa aikin noman shinkafa a wani bangare na kokarin inganta ayyukan yi da samar da abinci a yankin.

 

Da yake jawabi yayin bikin kaddamar da aikin aka gudanar a garin Babura, shugaban ya bayyana cewa, Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bullo da shirin a matsayin wani muhimmin mataki na samar da guraben ayyukan yi ga matasa, da habaka tattalin arzikin kananan hukumomi, da karfafa samar da abinci a fadin jihar.

 

A cewarsa, gwamnatin jihar ta samar da muhimman kayayyakin amfanin gona da suka hada da takin zamani, magungunan kashe kwari, irin shinkafa mai yawan gaske, da injinan feshi.

 

Malam Hamisu Garu ya yi nuni da cewa, za a raba kayayyakin ga matasa 200 da aka zabo daga sassa daban-daban na karamar hukumar.

 

Ya kara da cewa, karamar hukumar ta ware tare da share fili mai fadin hekta 100 domin fara aikin.

 

Shugaban ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin jihar da ta fara shirin.

 

Ya ce, shirin zai hana matasa yin kaura zuwa birane domin neman ayyukan yi, lamarin da yakan jefa su cikin hatsari da kuma gurgunta makomarsu.

 

A nasa jawabin, babban daraktan cibiyar bincike ta jiha Dakta Suleman Rufa’i, ya bayyana shirin a matsayin wani kokari na farko, inda ya kara da cewa akwai shirye-shiryen kara fadada shi bisa burin gwamnati na mayar da jihar Jigawa a matsayin jihar da ke kan gaba wajen samar da abinci a Nijeriya.

 

Rediyon Nijeriya ya ruwaito cewa, sarakunan gargajiya da suka halarci taron sun hada da Hakimin Babura, Sarkin Ban Ringim, Alhaji Muhammad Nata’ala Mustapha, da Hakimin Garu, Dan-makwayon Ringim, Alhaji Suhailu Abubakar Usman, sun yabawa gwamnati kan wannan shiri.

 

Shugabannin sun bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin su nuna kishin kasa da alhaki ta hanyar amfani da tallafin yadda ya kamata domin tabbatar da nasarar shirin.

 

USMAN MZ/Dutse

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot
  • Wa zai cire wa Real Madrid kitse a wuta?
  • An Share Filin Noma Kadada 100 Don Karfafa Matasa Su Yi Noma A Babura Jihar Jigawa
  • Kasar Yemen Ta Kakaba Takunkumi Kan Amurka A harkokin Fitar Da Man Fetur Din Kasarta
  • Shettima zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Gabon
  • Shettima zai tafi Gabon bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar
  • Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Gabon
  • Gwamnan Jigawa Ya Halarci Taron Ranar Ma’aikata Ta Bana