An kama mutane 1,611 da ƙwato motoci 21, babura 51 da aka sace a Abuja
Published: 2nd, May 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan birnin tarayya Abuja ta ce ta kama mutane 1,611 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka haɗa da safarar miyagun ƙwayoyi tare da ƙwato motocin sata guda 21, babura 51 da kuma miyagun ƙwayoyi.
Kwamishinan ’Yan sanda CP Ajoa Saka Adewale, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da motocin da aka ƙwato, baburan da sauran kayayyaki a gaban manema labarai a ranar Juma’a a Abuja.
Ya ce an kama mutane 16 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban na satar mota. Ya kuma ce shida daga cikin motoci 21 da aka ƙwato an mayar wa masu su bayan an tantance su, yayin da sauran motocin 13 ke nan a hannun rundunar.
Ya ce, rundunar ta kai samame da dama a wurare da dama, inda ta kama mutane 1,611 da ake zargi, inda ya ce da yawa daga cikinsu na da alaƙa da laifukan da suka shafi muggan ƙwayoyi da sauran miyagun ayyuka.
Adewale ya ce, an gano wasu adadi mai yawa na miyagun ƙwayoyi da tabar wiwi a yayin gudanar da samamen, waɗanda a halin yanzu ake tsare da su a matsayin baje kolin da za a ci gaba da gudanar da bincike da kuma gurfanar da su gaban ƙuliya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
Wasu mutum shida sun shiga hannun ’yan sanda kan zargin satar zinari da kuɗinta ya haura Naira miliyan 109.5 a Jihar Kebbi.
Sashen binciken manyan laifuka na rundunar ’yan sanda a jihar Kebbi na tuhumar su da sace sarkoƙin zinare guda biyar sauran kayan zinare daga wani gida a garin Ka’oje, Ƙaramar Hukumar Bagudo.
Sauran sun haɗa da zobba huɗu da munduwar hannu tara, da nauyinsu ya kai gram 782.7 — dukkansu mallakar ’ya’ya da ’yan uwar mai gidan.
Wanda ake tuhuma ya amsa laifiBayan samun koken, jami’an suka kama Ibrahim Abubakar Ka’oje, jami’i a Hukumar Gyaran Hali ta Kasa, wanda a yayin bincike, ya amsa laifin.
’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhuYa bayyana cewa ya sayar da kayan ga wasu mutane biyu, dukkansu daga Sakkwato, tare da wasu mutum biyu a Jihar Kebbi.
An kuma gano wanda ya taimaka masa wajen sayar da wasu daga cikin kayan, inda ya karɓi naira miliyan 2.5 a matsayin lada.
Rundunar ’yan sanda ta bayyana cewa har yanzu tana neman sauran da suka gudu, bisa zargin taimakawa wajen sayar da kayan sata.
Ana zargin an sayi filaye biyu a Birnin Kebbi da kuɗin da aka samu daga sayar da kayan.
Abubuwan da aka ƙwatoKayan da aka ƙwato sun haɗa da munduwar hannu biyu, babur ɗin Haouje, da kuma wayoyin iPhone 16, Samsung Galaxy Ultra da Samsung Flip.
Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya jinjina wa jajircewar jami’ansa bisa wannan nasara.
Ya kuma yi kira gare su da su ci gaba da aiki tukuru domin cafke sauran da ake nema da kuma ƙwato dukkan kayan da suka rage.