An kama mutane 1,611 da ƙwato motoci 21, babura 51 da aka sace a Abuja
Published: 2nd, May 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan birnin tarayya Abuja ta ce ta kama mutane 1,611 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka haɗa da safarar miyagun ƙwayoyi tare da ƙwato motocin sata guda 21, babura 51 da kuma miyagun ƙwayoyi.
Kwamishinan ’Yan sanda CP Ajoa Saka Adewale, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da motocin da aka ƙwato, baburan da sauran kayayyaki a gaban manema labarai a ranar Juma’a a Abuja.
Ya ce an kama mutane 16 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban na satar mota. Ya kuma ce shida daga cikin motoci 21 da aka ƙwato an mayar wa masu su bayan an tantance su, yayin da sauran motocin 13 ke nan a hannun rundunar.
Ya ce, rundunar ta kai samame da dama a wurare da dama, inda ta kama mutane 1,611 da ake zargi, inda ya ce da yawa daga cikinsu na da alaƙa da laifukan da suka shafi muggan ƙwayoyi da sauran miyagun ayyuka.
Adewale ya ce, an gano wasu adadi mai yawa na miyagun ƙwayoyi da tabar wiwi a yayin gudanar da samamen, waɗanda a halin yanzu ake tsare da su a matsayin baje kolin da za a ci gaba da gudanar da bincike da kuma gurfanar da su gaban ƙuliya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
A wani ɓangare na shirin gudanar da zaɓen cike gurbi na Babura/Garki a Majalisar Tarayya, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) reshen Babura ta shirya muhimmin taron masu ruwa da tsaki domin tabbatar da sahihin zaɓe mai inganci da haɗin kai.
A jawabinsa yayin taron, jami’in zaɓe na ƙaramar hukumar Babura, Malam Hafiz Khalid, ya gabatar da cikakken jadawalin ayyukan zaɓen.
Ya jaddada muhimmancin haɗin kai da gaskiya a kowane mataki, yana mai bayyana zaɓen a matsayin aikin gama gari da ke buƙatar goyon bayan duk masu ruwa da tsaki.
Mahalarta taron sun bayar da shawarwari masu amfani tare da gabatar da muhimman tambayoyi da suka shafi inganta sahihanci da nasarar zaɓen.
Wasu daga cikin batutuwan da aka tattauna sun haɗa da shirye-shiryen kayayyakin aiki, tsaro, wayar da kan masu zaɓe, da sauransu.
An kammala taron da sabunta ƙudurorin haɗin guiwa daga dukkan mahalarta, wajen tabbatar da gudanar da zaɓen cike gurbi cikin lumana, ‘yanci, adalci, da sahihanci a yankin Babura/Garki.
Wakilin Rediyon Najeriya ya bayyana cewa, taron da aka gudanar a ofishin INEC na Babura, ya samu halartar masu ruwa da tsaki da suka haɗa da Hakimin Babura, jami’an tsaro, wakilan jam’iyyun siyasa, jami’ai daga Ƙungiyar Direbobin Ƙasa (NURTW), Ƙungiyar Masu Motocin Haya (NARTO), ƙungiyoyin farar hula (CBOs), da sauran jami’an INEC.
Usman Muhammad Zaria