Aminiya:
2025-05-03@04:32:14 GMT

An kama mutane 1,611 da ƙwato motoci 21, babura 51 da aka sace a Abuja

Published: 2nd, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan birnin tarayya Abuja ta ce ta kama mutane 1,611 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka haɗa da safarar miyagun ƙwayoyi tare da ƙwato motocin sata guda 21, babura 51 da kuma miyagun ƙwayoyi.

Kwamishinan ’Yan sanda CP Ajoa Saka Adewale, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da motocin da aka ƙwato, baburan da sauran kayayyaki a gaban manema labarai a ranar Juma’a a Abuja.

Sarki Sanusi II ya naɗa sabon Galadiman Kano da wasu 4 Ra’ayin Jama’a kan ziyarar Tinubu Katsina

Ya ce an kama mutane 16 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban na satar mota. Ya kuma ce shida daga cikin motoci 21 da aka ƙwato an mayar wa masu su bayan an tantance su, yayin da sauran motocin 13 ke nan a hannun rundunar.

Ya ce, rundunar ta kai samame da dama a wurare da dama, inda ta kama mutane 1,611 da ake zargi, inda ya ce da yawa daga cikinsu na da alaƙa da laifukan da suka shafi muggan ƙwayoyi da sauran miyagun ayyuka.

Adewale ya ce, an gano wasu adadi mai yawa na miyagun ƙwayoyi da tabar wiwi a yayin gudanar da samamen, waɗanda a halin yanzu ake tsare da su a matsayin baje kolin da za a ci gaba da gudanar da bincike da kuma gurfanar da su gaban ƙuliya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Barayi

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi

Haka kuma Wang ya halarci taron ministocin waje na kasashe mambobin kungiyar BRICS da na kasashe kawayensu a wannan rana, inda aka tattauna game da yadda za a karfafa ra’ayin cudanyar bangarori daban daban.

 

Wang ya bayyana cewa, mafitar matsalolin da ake fuskanta a duniya ita ce kiyayewa da aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori daban daban. Ya ce bayan da ta habaka mambobinta, ya kamata kungiyar BRICS ta ci gaba yayata manufar yin shawarwari da juna da tabbatar da ci gaban juna da cin moriya tare, da kiyaye muhimman ka’idojin huldar kasa da kasa, da kuma kare tsarin ciniki tsakanin bangarori daban daban.

 

Wang ya jadadda cewa, amsar da Sin ta bayar game da yakin cinikayya a bayyane take, wato idan an dage kan yakin, ko kadan ba za mu ja da baya ba. Idan an shirya tattaunawa, dole ne mu girmama juna tare da yin zaman daidaito da juna. Ba don hakkinta na kanta ba ne, kasar Sin tana kuma kiyaye muradun bai daya na dukkanin kasashe. Abun da kasar Sin ke kiyayewa ba kawai hadin gwiwar cin moriyar juna ba ne, har ma da ka’idojin kasa da kasa. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Wani Babban Jami’in Sojan Kasar Burtaniya A Najeriya Tare Da Zarginsa Da Shigo Da Makamai
  • HOTUNA: Yadda aka baje kolin kayan laifin da ’yan sanda suka kama a Abuja
  • ’Yan acaba sun yi wa mai fura fyaɗe Abuja
  • ’Yan fashin teku sun sace mata 4 a hanyar ruwa na Bayelsa
  • Kamala Harris Ta Zargi Trump Da Haddasa Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi
  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna