Layukan Dogo Na Kasar Sin Sun Gudanar Da Sufurin Miliyoyin Fasinjoji A Ranar Farko Ta Hutun ‘Yan Kwadago
Published: 2nd, May 2025 GMT
Layukan dogo na kasar Sin sun gudanar da sufurin kusan fasinjoji miliyan 23.12 a jiya Alhamis, ranar farko ta bikin ranar ‘yan kwadago ta duniya da aka saba yi duk shekara a watan Mayu, kamar yadda kamfanin sufurin layin dogo na kasar Sin ya bayyana.
A cewar alkaluman da kamfanin ya fitar a yau Jumma’a, wannan adadi ya nuna karuwar kashi 11.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Amurka ta sake kai Hari a yankunan Saada da Hudaidah na Yemen
Jiragen yakin Amurka sun sake kai hare-hare da dama kan lardunan Saada da Hudaidah na kasar Yemen yau Alhamis.
Wata majiyar tsaro a Yemen ta kara da cewa, an kai wasu hare-hare uku a yankin Kataf da ke lardin Saada, yayin da wani kuma ya afkawa gundumar al-Houk da ke lardin Hudaidah a gabar tekun yammacin Yeman, lamarin da ya janyo hasarar kayayyaki na fararen hula.
Dama a cewar kafar yada labaran kasar Yemen Al-Masirah, jiragen yakin Amurka sun kai hari a gundumar al-Sayl da ke lardin al-Jawf a arewacin kasar Yemen ranar Laraba.
Tun a ranar 15 ga watan Maris da ya gabata ne, kawencen Amurka da Birtaniya ke kai hare-hare ta sama kan kasar Yamen, domin nuna goyon baya ga gwamnatin Isra’ila.
Kafin hakan a ranar Litinin, 28 ga watan Afrilu, Amurka ta kai wani mummunan hari ta sama a birnin Sanaa, inda ta kashe mutane akalla 12 tare da jikkata wasu hudu.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta kasar Yemen ta fitar ta ce an kashe ‘yan kasar Yemen 12 da suka hada da kananan yara, yayin da wasu hudu suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai kan wasu gidajen zama a yankin Thaqban na birnin Sanaa.
A safiyar litinin jiragen yakin Amurka sun kai harin bam a daya daga cikin wuraren da ake tsare da bakin haure ‘yan Afirka da ke yankin Saada, inda suka kashe mutane 68 tare da jikkata 47.