Aminiya:
2025-08-01@20:23:10 GMT

Sarki Sanusi ya naɗa sabon Galadiman Kano da wasu 4

Published: 2nd, May 2025 GMT

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya naɗa Alhaji Munir Sanusi Bayero a matsayin sabon Galadiman Kano, tare da wasu manyan muƙamai guda huɗu.

Sauran waɗanda aka naɗa sun haɗa da Alhaji Kabir Tijjani Hashim, Hakimin Nassarawa, wanda ya zama sabon Wamban Kano; Alhaji Mahmud Ado Bayero Hakimin Gwale, wanda aka naɗa a matsayin Turakin Kano; Adam Lamido Sanusi a matsayin Tafidan Kano; da Alhaji Ahmad Abbas Sanusi a matsayin Yariman Kano.

Ra’ayin Jama’a kan ziyarar Tinubu Katsina Gobarar rumbum makamai Maiduguri da Matakan da ya kamata a ɗauka — Ƙwararru

Da yake jawabi yayin bikin naɗin sarautar, Sarki Sanusi ya buƙaci sabbin masu riƙe da muƙaman da su kasance masu koyi da shugabanni da kuma ci gaba da kare martabar sarautar, tawali’u da tausayi ga jama’a.

“An zaɓo ku ne bisa la’akari da tarihinku da na iyalan ku, mafi yawanku kun nuna biyayyar ku ga Masarautu da zuriyarmu kuma kun bayar da gudunmawa sosai wajen tallafa wa talakawa da ci gaban al’umma, ina roƙonku da ku yi koyi da magabatanku, Allah Ya yi muku jagora wajen gudanar da ayyukanku,” in ji shi.

Taron wanda ya gudana a fadar Sarkin ranar Juma’a ya samu halartar Gwamna Abba Kabir Yusuf da ’yan majalisar zartarwa na jiha da shugabannin gargajiya da na addini da ’yan uwa da sauran masu faɗa a ji.

A wani lamari makamancin haka, Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, shi ma ya naɗa Alhaji Sunusi Lamido Ado Bayero a matsayin Galadiman Kano a ƙaramar fadar Nassarawa.

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Munir Sanusi Bayero Sarki Sanusi II

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu

Allah Ya yi wa Mai Martaba, Sarkin Gudi Alhaji Isa Bunuwo Ibn Khaji rasuwa a asibitin Nizameye da ke Abuja ranar Alhamis.

Mai martaba Sarkin wanda ke garin Gadaka a Ƙaramar hukumar Fika cikin Jihar Yobe ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya.

Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana

Sakataren masarautar Gudi da ke Gadaka ne ya tabbatar da rasuwar Sarkin, ya kuma ce an shirya gudanar da Sallar Jana’izar marigayi Sarkin a ranar Juma’a da ƙarfe 2:00 na rana a fadar Sarkin da ke Gadaka.

Labarin rasuwar Sarkin dai ya tayar da hankalin a ɗaukacin al’ummar masarautar da ma Jihar Yobe baki ɗaya, inda da yawa ke jinjinawa jagorancinsa da kuma abin da ya bari.

Ana ci gaba da miƙa saƙon ta’aziyyarsu daga ko’ina, a dai-dai lokacin da jama’a ke juyayin rashin Sarkin.

Marigayi Sarkin Gudi ya shahara wajen hikima da jagoranci da jajircewa wajen ci gaban al’ummarsa tare da  taka muhimmiyar rawa wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da haɗin kai a tsakanin al’umma, kuma za a riƙa tunawa da abin da ya bari har zuwa tsawan lokaci.

Sallar jana’izar wadda manyan malamai za su jagoranta, za ta samu halartar manyan baƙi, shugabannin gargajiya da sauran al’umma.

Za a binne gawar Sarkin kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a garin na Gadaka.

Al’ummar masarautar dai na cikin alhini, inda da dama ke nuna alhininsu dangane da rashin jagoransu.

Ana sa ran gwamnati da al’ummar Jihar Yobe za su yi wa marigayi Sarkin gaisuwar ban girma, ganin irin rawar da ya taka wajen samar da zaman lafiya da ci gaba a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
  • Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu
  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi