Aminiya:
2025-05-03@03:55:38 GMT

Sarki Sanusi ya naɗa sabon Galadiman Kano da wasu 4

Published: 2nd, May 2025 GMT

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya naɗa Alhaji Munir Sanusi Bayero a matsayin sabon Galadiman Kano, tare da wasu manyan muƙamai guda huɗu.

Sauran waɗanda aka naɗa sun haɗa da Alhaji Kabir Tijjani Hashim, Hakimin Nassarawa, wanda ya zama sabon Wamban Kano; Alhaji Mahmud Ado Bayero Hakimin Gwale, wanda aka naɗa a matsayin Turakin Kano; Adam Lamido Sanusi a matsayin Tafidan Kano; da Alhaji Ahmad Abbas Sanusi a matsayin Yariman Kano.

Ra’ayin Jama’a kan ziyarar Tinubu Katsina Gobarar rumbum makamai Maiduguri da Matakan da ya kamata a ɗauka — Ƙwararru

Da yake jawabi yayin bikin naɗin sarautar, Sarki Sanusi ya buƙaci sabbin masu riƙe da muƙaman da su kasance masu koyi da shugabanni da kuma ci gaba da kare martabar sarautar, tawali’u da tausayi ga jama’a.

“An zaɓo ku ne bisa la’akari da tarihinku da na iyalan ku, mafi yawanku kun nuna biyayyar ku ga Masarautu da zuriyarmu kuma kun bayar da gudunmawa sosai wajen tallafa wa talakawa da ci gaban al’umma, ina roƙonku da ku yi koyi da magabatanku, Allah Ya yi muku jagora wajen gudanar da ayyukanku,” in ji shi.

Taron wanda ya gudana a fadar Sarkin ranar Juma’a ya samu halartar Gwamna Abba Kabir Yusuf da ’yan majalisar zartarwa na jiha da shugabannin gargajiya da na addini da ’yan uwa da sauran masu faɗa a ji.

A wani lamari makamancin haka, Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, shi ma ya naɗa Alhaji Sunusi Lamido Ado Bayero a matsayin Galadiman Kano a ƙaramar fadar Nassarawa.

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alhaji Munir Sanusi Bayero Sarki Sanusi II

এছাড়াও পড়ুন:

An Bada Gudummawar Kekunan ga Masu Bukatu Na Musamman A Birnin Kebbi.

Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu tare da hadin guiwar Kyakyawar Gate Handicapped Centre Jos, sun bayar da tallafin keken guragu guda dari da talatin ga masu bukata ta musamman a Birnin Kebbi na jihar Kebbi.

 

Kakakin Ministan, Sadiq Nura Maiyaka, ya ce Ministan ya kuduri aniyar taimakawa masu bukata ta musamman don gudanar da ayyukansu na yau da kullun da sauran jama’a.

 

Ya shawarci wadanda suka amfana da su yi amfani da keken guragu kada su sayar da su domin su rika zagayawa da ayyukansu ba tare da wata damuwa ba.

 

Daraktan yada labarai na Kyawawan Gate Handicapped Centre Jos, Sandra Riliwan, ta ce wannan ba shi ne karon farko da cibiyar ke hada kai da masu hannu da shuni da kungiyoyi ba don taimakawa masu bukata ta musamman a jihar Kebbi.

 

Don haka ta bukaci karin abokan hulda domin su taimaka ma masu bukata ta musamman ba a jihar Kebbi kadai ba har ma da kasa baki daya da kuma wajenta.

 

Ita ma wata mai gabatar da shirin kuma wata malama daga Makarantar Sakandaren ’Yan Mata ta Dokta Amina ta Jihar Kebbi, Halima Danjuma Fatauci, ta ce ta ji takaicin yadda wasu ke gurgunta yunkurin da suke yi ba tare da taimakon masu hannu da shuni ba, ta kuma yanke shawarar bayar da gudunmuwar wata-wata domin ta taimaka wa wasu da keken guragu domin su yi tafiya cikin sauki.

 

Ta godewa Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu da Cibiyar Nakasassu ta Jos bisa amincewa da bukatarta ta hanyar bayar da tallafin keken guragu 130 ga masu bukata ta musamman a jihar Kebbi.

 

COV/ Abdullahi Tukur

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara Ta Ƙone Shaguna 3 Da Kayayyaki Masu Yawan Gaske A Ibadan
  • An Cafke Saurayi Bisa Zargin Yi Wa ‘Yar Budurwarsa Fyade A Bauchi
  • Gwamnan Jigawa Ya Halarci Taron Ranar Ma’aikata Ta Bana
  • An Bada Gudummawar Kekunan ga Masu Bukatu Na Musamman A Birnin Kebbi.
  • Dakarun IRGC Na JMI Sun Kaddamar Da Sabon Kwale-Kwale Mai Cilla Makamai Masu Linzami
  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  •  Manyan Malaman Roman Katolika Sun Fara Taron Zabar Paparoma