Gwamnatin jihar Zamfara ta kammala biyan sama da naira biliyan 13 na garatuti, wanda ke nuna wani gagarumin mataki na inganta jin dadin ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya a jihar.

 

Mataimakin gwamnan jihar, Mani Malam Mummuni, ya bayyana hakan a yayin bikin ranar ma’aikata na shekarar 2025 da aka gudanar a Gusau, babban birnin jihar.

 

A cewar Mummuni, gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta jajirce wajen ganin ta magance kalubalen da ma’aikata da masu ritaya ke fuskanta a jihar.

 

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar tana sane da korafin ma’aikatan da aka yi kuskuren cire su daga lissafin albashin sakamakon aikin tantance ma’aikatan da aka kammala.

 

“Gwamnati ta riga ta kafa wani kwamiti a karkashin jagorancin shugaban ma’aikatan don shawo kan lamarin, muna da yakinin za a kammala hakan nan ba da dadewa ba.”

 

Mataimakin gwamnan ya kuma bayyana cewa, bisa la’akari da muhimmiyar rawar da ma’aikata ke takawa, gwamnatin Lawal ta dauki kwakkwaran matakai na kyautata jin dadinsu da yanayin aikinsu.

 

“A wani bangare na wannan kokarin, mun fara aiwatar da sabon mafi karancin albashi na N70,000 ga ma’aikatan gwamnati.

 

Mummuni ya ci gaba da bayanin cewa, bayan albashi, gwamnatin ta ba da kulawa ta musamman ga halin da ‘yan fansho maza da mata ke ciki wadanda suka sadaukar da shekaru da dama wajen yi wa jihar hidima.

 

Ya kuma amsa bukatun ma’aikata dangane da karin girma, inda ya bayyana cewa ana magance batun aiwatar da karin girma, musamman ga wadanda ke da karin girma ko sama da haka ba tare da daidaita albashi ba.”

 

“A wannan rana ta musamman, ina jinjina wa juriya da jajircewa da ma’aikatan Zamfara suke yi, ina yaba wa jajircewarku, Allah Ya saka muku da alheri,” ya kammala.

 

Tun da farko, Shugaban kungiyar ‘yan kasuwa (TUC), Majalisar Jihar Zamfara, Kwamared Sa’idu Mudi, ya roki gwamnati da ta magance matsalolin da ma’aikata ke fuskanta.

 

Wadannan sun hada da cikakken aiwatar da sabon mafi karancin albashi, sakin tsarin albashin da aka amince da shi, sake duba kudaden fansho, da maido da ma’aikatan da aka yi kuskuren cire su daga lissafin albashi.

 

Kwamared Mudi, ya yabawa gwamnatin jiha bisa nasarorin da ta samu kamar gaggauta biyan albashi da fansho, da kuma biyan kashi 30% na albashin ma’aikatan gwamnati a fadin kananan hukumomin a matsayin kari na wata 13.

 

Shima da yake jawabi a wajen taron, shugaban kungiyar kwadago ta kasa NLC reshen jihar Zamfara, Kwamared Sani Halliru, ya jaddada muhimmancin ranar ma’aikata wajen ganin irin gwagwarmayar da ma’aikata da kungiyoyin kwadago ke yi na samar da ingantacciyar yanayin aiki.

 

Ya koka da cewa ba a sake duba kudaden fansho na wata-wata ba a cikin shekaru 27 da suka gabata, sabanin dokar fansho da ta tanadi sake duba duk shekara biyar.

 

“Mai girma gwamna, la’akari da cewa ma’aikatan Zamfara ba sa cikin wani shiri na fensho, muna kira ga gwamnati da ta gaggauta aiwatar da tsarin fansho mai dorewa.”

 

Yayin da yake yaba kokarin gwamnati na yaki da rashin tsaro, ya bukaci hukumomi da kada su sassauta, domin rashin tsaro ya kasance babbar barazana a jihar.

 

Ya kuma yi kira ga sauran ma’aikata da su gudanar da bukukuwan farin ciki tare da karfafa musu gwiwa da su ci gaba da jajircewa da kuma riko da ayyukansu na tallafa wa ci gaban jihar Zamfara.

 

 

COV/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo

Hukumar kula da da’ar ma’aikata ta sanar da cewa, a halin yanzu ana iya  bayyana kadarorin ma’aikatan ta hanyar yanar gizo, wani mataki da aka tsara domin saukaka aikin da kuma kara yin lissafi.

 

Daraktan ofishin na jihar Jigawa Abubakar Bello ne ya bayyana haka a lokacin da ya ziyarci shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Muhammad K. Dagaceri a ofishin sa.

 

Abubakar Bello ya jaddada cewa sabon shirin na da nufin rage dinbin aikin dake gaban ma’aiakata da kuma saukaka tantance kadarorin domin yaki da cin hanci da rashawa a cikin tsarin.

 

“Mun sauya dabara zuwa rajista ta yanar gizo don bayyana kadarorin, muna ba wa mutane damar kammala aikin daga gidajensu. Duk da haka, muna neman goyon bayan ku don tabbatar da cewa an sanar da jami’an gwamnati tare da karfafa gwiwar su bi wannan sabon tsari,” in ji shi.

 

Da yake mayar da jawabi, shugaban ma’aikata na jiha Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ya yi alkawarin wayar da kan jami’an gwamnati cikin tsanaki game da muhimmancin bayyana kadarorin su, kamar yadda hukumar da’ar ma’aikata ta ba su umarni.

 

Ya tunatar da cewa rashin yin biyayya ga kundin tsarin mulkin kasa ne.

 

Dagaceri ya bada tabbacin bada goyon baya da hadin kai domin cimma burin da ake so na wannan shiri.

 

USMAN MZ

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN
  • Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul
  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau