Ya ce, “Muddin muna da kwarin gwiwa, da karfin goyon bayan juna da hadin kai, za mu kai ga kawar da manufofi masu illa, da wanzar da daidaito da ci gaba a manufofin jagoranci a fannin kare yanayi da samar da ci gaba. ” (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe ta rattaba hannu kan kwangilar biliyan 48 na aikin zaizayar Kasa

Jihar Gombe ta rattaba hannu kan kwangilar sama da biliyan 48 don aikin kula da Makarantar ‘yan mata ta Mega dake Doma da kuma zaizayar kasa

 

Baya ga sanya hannu kan kwangilar, an kuma bayar da cak don biyan diyya ga mazauna yankin mai nisan mita 10 da ke kan hanyar aikin.

 

Da yake jawabi a wurin rattaba hannu kan kwangilar a hukumance a Hayin Missau Bogo, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matakin a matsayin wani muhimmin mataki na tabbatar da muhallin Gombe da kuma kare makomar jama’a.

 

A cewarsa aikin ba wai kawai zai shawo kan zaizayar kasa ba ne zai dawo da fata ga al’ummomin da abin ya shafa.

 

Alh. Inuwa Yahaya wanda ya bada umarnin kammala aikin a cikin watanni 30 ya bukaci dan kwangilar da ya gabatar da aiki mai inganci.

 

Ya yi kira ga sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma da su ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen wanzar da zaman lafiya da juna a tsakanin al’umma, da kuma kiyaye ayyukan da ba su dace ba kamar sare itatuwa da zubar da shara da ke cutar da muhalli.

 

Shima da yake jawabi kwamishinan albarkatun ruwa da muhalli da gandun daji na jihar Gombe Mal. Muhammad Fawu, ya yabawa hadin gwiwar da gwamnatin Gombe da Bankin Duniya suka yi wajen samar da kudaden aikin, ya ce wani gagarumin kokari ne na kare muhalli da kuma tabbatar da makomar al’umma.

KARSHEN HUDU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje
  • Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
  • Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
  • Limamin Sallar Juma’ar Tehran Ya Jaddada Cewa: Babu Wanda Zai Dakatar Da Iran Tace Sinadarin  Uranium
  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran
  • Brazil Ta Goyi Bayan Iran Kan Hakkinta Na Mallakar Makamashin Nukiliya
  • Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda
  • AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika
  • Gwamnatin Gombe ta rattaba hannu kan kwangilar biliyan 48 na aikin zaizayar Kasa
  • NEJERIYA A YAU: Sai Yaushe ’Yan Najeriya Za Su Ci Gajiyar Manufofin Shugaba Tinubu?