Shugaba Xi Ya Jaddada Aniyar Kasarsa Ta Goyon Bayan Kudurorin Kyautata Yanayi Da Ci Gaba Marar Gurbata Muhalli
Published: 24th, April 2025 GMT
Ya ce, “Muddin muna da kwarin gwiwa, da karfin goyon bayan juna da hadin kai, za mu kai ga kawar da manufofi masu illa, da wanzar da daidaito da ci gaba a manufofin jagoranci a fannin kare yanayi da samar da ci gaba. ” (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
Shugaba Masoud Pezeshkian ya yi watsi da hankoron Amurka na tunzura kawayenta, musamman gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila, na yunkurin kawo karshen shirin nukiliyar Iran.
Shugaban an Iran ya bayyana hakan ne yayin wata hira da gidan talabijin na Aljazeera na kasar Qatar a wannan Talata, inda ya bayyana cewa, za a ci gaba da inganta sinadarin Uranium a kasar Iran nan gaba bisa tsarin dokokin kasa da kasa.
Wannan yunkuri yasa an ga bangarorin biyu na Amurka da Isra’ila suna matsa lamba a kan sauran bangarori na duniya, tare da bayyana Shirin na Iran a matsayin mai matukar hadari ga duniya, da nufin samun goyon bayan kasashen duniya kan bakaken manufofisu a kan kasar ta Iran.
Dangane da zargin da shugaban Amurka Donald Trump ya yi kan Shirin Iran da kuma neman samoma kansa hujjoji na kaiwa Iran hari, da kuma bayyana cewa harin Amurka ya kawo karshen Shirin Iran na nukiliya, Pezeshkian ya ce, “Da’awar cewa shirinmu na nukiliya ya kawo karshe, batu ne na yaudara.”
“Ilimin nukiliya yana a cikin kwakwalen masananmu ne na kimiyyarmu, ba a cikin wurarenmu ba.” In ji Pezeshkian.
Haka nan kuma shugaban na Iran ya sake nanata matakin kin amincewa da zargin kasarsa da hakoron kera makaman kare dangi, da kuma kara jaddada matsayin kasar na ci gaba da daukar matakan da take yi wajen kara inganta shirinta na makamashin nukiliya domin ayyukan farar hula.
Pezeshkian ya kuma sake nanata shirye-shiryen Iran na yin shawarwarin da ba su ginu a kan haramtawa Iran hakkinta na inganta na tace sanadarin Uranium ba, amma ya ce “duk wata tattaunawa da za a yi a nan gaba dole ne ta dogara a kan batutuwa na masu tabbatar da hakkokin Iran.