Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya
Published: 23rd, April 2025 GMT
Wata ƙungiyar masu iƙirarin jihadi da ake kira Mahmuda tana ci gaba da kafuwa da ƙara ƙarfi tare da addabar jama’a a wasu garuruwa na ƙananan hukumomin Ilesha Baruba da Kemaanji da Kaiama da Baruten na Jihar Kwara.
Bayanai sun ce ’yan ƙungiyar sun sami mafaka ne a gandun dajin Kainji Lake National Park, kuma daga can ne suke kai hare-hare a garuruwan da ke makwabtaka da dajin har ma da wasu sassa na Jihar Neja.
Bayanai sun ce ko a Juma’ar da gabata sai da mayaƙan suka kashe wasu fulani huɗu, ɗan sa-kai da wani saurayi mai shekaru 19.
Aminiya ta ruwaito cewa ’yan ta’addan da suka yi shiga ta kakin soji haye a kan babura sun kai harin ne yayin da ake tsaka da cin wata kasuwar dare, inda suka buɗe wuta kan mai uwa da wabi sannan suka arce.
Rahotanni na cewa sabuwar ƙungiyar tana kashe-kashe da garkuwa da mutane a ƙauyukan Kemaanji, Tenebo, Baabete, Nuku, da Nanu a ƙananan hukumomin Kaiama da kuma yankunan Yashikira na Ƙaramar Hukumar Baruten gami da yankunan Babana da Wawa da ke Ƙaramar Hukumar Borgu ta Jihar Neja.
‘Za mu tabbatar da tsaro a yankin Gandun Daji na Kainji’Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq yayin wata ziyara da kai wuraren da abin ya shafa tare da manyan jami’an tsaro, ya ce ’yan ta’addan na kai wa ’yan sa-kai harin ne a matsayin ramuwar gayya saboda matsin lambar da suke yi musu.
Da kuma yake jawabi a fadar Sarkin Kaiama, Alhaji Muazu Shehu Omar, gwamnan ya ce za su yi duk mai yiwuwa tare da sojoji da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da tsaro da dawo da zaman lafiya a yankin Gandun Daji na Kainji.
Yanzu haka dai mutanen garuruwan da abin ya shafa suna ta yin hijira zuwa wasu wurare, domin guje wa ƙwazzabar ’yan ƙungiyar ta Mahmuda.
Mazauna yankin sun ce dama can ’yan ƙungiyar ta Mahmuda ta taɓa kafa sansani a ƙananan hukumomin Kaiama da Baruten, inda suka nuna cewa babu ruwansu da mutanen gari kuma hakan ya sa mutanen suka saki jiki da su.
Mazauna sun ce da farko Mahmudawan sun soma yaɗa da’awa ta Musulunci, amma daga baya suka fara ɗaukar wasu matasa a matsayin mayaƙa da masu tattaro musu bayanai.
Wani mazaunin yankin ya ce daga baya ne Mahmudawan suka fara yawo da makamai suna kama mutanen gari da kuma yanke musu hukunci har ma da kashe wasu. “Sun fi shekara 5 da fara bayyana”
Ya ƙara da cewa a wannan karon da suka dawo ”Daga gabas da gari zuwa yamma, mutum baya da halin zuwa gona mai nisan kilomita biyu haka.
“Gaba ɗaya na tsorata, kashi 50 cikin ɗari na mutanen gari sun gudu.”
Haka nan kuma ƙungiyar ta Mahmuda ta haramta wa mutanen Kaiama da Baruten noma “kashi 95 cikin 100 na mutanenmu manoma ne.
“To yanzu sun ce ba mu da damar yin noman ka ga dai yanzu mutuwa ta fuskance mu, ba ma yunwa ba.”
“Mun sha ankarar da mahukunta kan ayyukan ’yan ƙungiyar amma ba a ɗauki mataki ba, amma sai a kwanan ne sojoji suka yi musu ruwan wuta a maboyarsu, in ji wani mazauni, Haruna Idirissa.
Wasu rahotanni na cewa ’yan ƙungiyar wani tsagi ne na ƙungiyar Boko Haram da Abubakar Shekau ya jagoranta, da suka fito daga wani sashe na ƙasashen Benin da Nijar, sai dai suna da sassaucin tsaurin ra’ayi.
Mun tanadi tsaro — ’Yan sandaTuni dai Kakakin rundunar ’yan sandan Kwara, Adetoun Ejire-Adeyemi a wata sanarwa da ya fitar, ya musanta ɓullar ƙungiyar, yana mai cewa ko labarin da ake yaɗawa na cewa sun kashe ’yan sa-kai 15 ba gaskiya ba ne.
Sai dai rundunar ta bai wa mazauna tabbacin tanadar tsaro ingantacce domin wanzar da zaman lafiya.
Rundunar ta kuma buƙaci mazauna da su ci gaba da bayar da haɗin kai ta hanyar kiyaye duk wata doka, tana mai kiran da su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba tare da wata fargaba ba.
Muna zaune cikin fargaba —BasarakeSarkin Yashikira, Alhaji Umaru Seriki, ya bayyana cewa a yanzu haka suna zaune cikin fargaba saboda ta’adar sabuwar ƙungiyar da ke musu barazana a kodayaushe.
Tun a shekarar 2022 Majalisar Dattawa ta bayyana fargabaA shekarar 2022 ce Majalisar Dattawa ta yi iƙirarin cewa sabuwar ƙungiyar ta samu mafaka a wasu ƙananan hukumomi uku na jihohin Kwara da Neja.
Majalisar Dattawan a wancan lokacin ta yi kira da babbar murya, inda ta nemi hukumomin tsaro da su ɗauki ƙwararan matakai kan ’yan bindigar da duk wani ɓurɓurshi na miyagu da ke addabar yankin Gandun Daji na Kainji.
Aminiya ta ruwaito cewa, Sanatan Kwara ta Tsakiya, Sadiq Umar tare da Mataimakin Bulaliyar Majalisar, Sanata Aliyu Abdullahi mai wakiltar Neja ta Arewa ne suka gabatar da wannan ƙudiri.
A watan jiya ne ƙwararren mai sharhi kan yaƙi da tayar da ƙayar baya, Zagazola Makama, ya ba da rahoton cewa ’yan sa-kai sun kama wani ɗan bindiga da ya bayar da bayanan sirri kan ayyukan ƙungiyar.
A halin yanzu dai bayan ɓullar Mahmudawa, ƙungiyoyin ta’adda masu tayar da ƙayar baya na ci gaba da ƙaruwa a ƙasar.
Ƙungiyoyin ta’addan da ake fama da su a Nijeriya sun haɗa da Boko Haram, ISWAP, Lakurawa, Ansaru da kuma ta bayan nan Mahmuda.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ISWAP Lakurawa yan ƙungiyar ƙungiyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Ya ƙara da cewa ‘yan’uwa da abokan arziƙi da suka shirya wannan biki na karrama Farfesa Armaya’u Bichi tare da bashi lambar yabo tare da wasu muhimman mutane waɗanda suka taimaimake shi wajen gudanar da shugabanci sun kyauta sannan sun ajiye ƙwarya a gurbinta.
Shima da yake gabatar da jawabinsa, shugaban riƙo na jami’ar gwamnatin Tarayya dake Katsina (FUDMA), Farfesa Aminu Ado ya ce Bichi mutum ne mai jin tausayin al’umma musamman mutanen dake ƙarƙashinsa.
Farfesa Ado ya ce har ƙasa ta naɗe ba zai mance da irin gagarumin ci gaban da Farfesa Arma’yau ya kawo ma jami’ar FUDMA ba.
Haka kuma a yayin bikin an ƙaddamar da littafin waƙoƙin da wasu mawaƙa suka yi wa tsohon shugaban na FUDMA mai suna ‘MALAMI A BAKIN MAWAƘA,’ wanda wasu ma’aikatan jami’ar suka rubuta.
Babban mai ƙaddamar da littafin, kuma shugaban ƙungiyar Jami’oin Afrika masu zaman kansu, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo wanda ya samu wakilcin Dakta Ali Yusuf Kakaki ya sa ya sayi kwafi biyu a kan naira miliyan biyu (N2, 000, 000), sai kuma Sanata Alu Magatakardan Wamako ya sayi kwafi uku kan naira miliyan ɗaya.
Frafesa Armaya’u Bichi, ya nuna godiyarsa ga waɗanda suka shirya wannan taron domin taya shi murnar kammala aiki lafiya. Tare da jinjina da fatan alheri ga kafatanin waɗanda suka samu damar halartar wannan taro.
A yayin taron An karrama Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da shi kansa Farfesa Armaya’u Bichi da Farfesa Abubakar Rasheed da Malam Rufa’i Bichi da Malam Adamu Adamu, tsohon ministan ilimi a zamanin mulkin Buhari.
ranar Asabar 13 ga watan Satumban 2025 makusantan tsohon shugaban jami’ar Gwamnatin Tarayya dake Dutsinma ta jihar Katsina, Farfesa Armaya’u Hamisu Bichi sun gudanar da gagarumin taron murna da farin cikin kammala aiki lafiya tare da karrama shugaban rukunin jami’oin Maryam Abacha American University, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da lamar yabo.
Gagarumin bikin wanda aka gudanar da shi a babban ɗakin taro na kwalejin ilimi na Tarayya (FCE) Bichi ya samu halartar ɗimbin masoya daga ko’ina a faɗin Nijeriya.
Farfesa Abubakar Adamu Rasheed tsohon shugaban Hukumar dake kula da jami’oin ƙasa (NUC), a yayin da yake jawabi ya bayyana Farfesa Armaya’u a matsayin mutumin kirki mai tausayi da ƙaunar jama’a.
Ya ƙara da cewa ‘yan’uwa da abokan arziƙi da suka shirya wannan biki na karrama Farfesa Armaya’u Bichi tare da bashi lambar yabo tare da wasu muhimman mutane waɗanda suka taimaimake shi wajen gudanar da shugabanci sun kyauta sannan sun ajiye ƙwarya a gurbinta.
Shima da yake gabatar da jawabinsa, shugaban riƙo na jami’ar gwamnatin Tarayya dake Katsina (FUDMA), Farfesa Aminu Ado ya ce Bichi mutum ne mai jin tausayin al’umma musamman mutanen dake ƙarƙashinsa.
Farfesa Ado ya ce har ƙasa ta naɗe ba zai mance da irin gagarumin ci gaban da Farfesa Arma’yau ya kawo ma jami’ar FUDMA ba.
Haka kuma a yayin bikin an ƙaddamar da littafin waƙoƙin da wasu mawaƙa suka yi wa tsohon shugaban na FUDMA mai suna ‘MALAMI A BAKIN MAWAƘA,’ wanda wasu ma’aikatan jami’ar suka rubuta.
Babban mai ƙaddamar da littafin, kuma shugaban ƙungiyar Jami’oin Afrika masu zaman kansu, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo wanda ya samu wakilcin Dakta Ali Yusuf Kakaki ya sa ya sayi kwafi biyu a kan naira miliyan biyu (N2, 000, 000), sai kuma Sanata Alu Magatakardan Wamako ya sayi kwafi uku kan naira miliyan ɗaya.
Frafesa Armaya’u Bichi, ya nuna godiyarsa ga waɗanda suka shirya wannan taron domin taya shi murnar kammala aiki lafiya. Tare da jinjina da fatan alheri ga kafatanin waɗanda suka samu damar halartar wannan taro.
A yayin taron An karrama Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo da shi kansa Farfesa Armaya’u Bichi da Farfesa Abubakar Rasheed da Malam Rufa’i Bichi da Malam Adamu Adamu, tsohon ministan ilimi a zamanin mulkin Buhari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp