Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci
Published: 19th, April 2025 GMT
Makera, Jihar Kaduna – Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Yusuf Dahiru Liman, ya halarci bukukuwan Easter tare da al’ummomin Kiristoci na Gundumar Makera, inda ya bukaci su yi amfani da lokacin wajen tabbatar sa saƙon bangaskiya, yabo, da sadaukarwa da ke tattare da bikin.
A jawabin da ya gabatar, Hon.
Kakakin ya kuma yi kira ga daukacin jama’ar Jihar Kaduna da su ci gaba da bunkasa zaman lafiya da juna ba tare da la’akari da bambancin addini, kabila ko ra’ayin siyasa ba, yana mai cewa hadin kai shi ne ginshikin ci gaban jihar da kasa baki daya. Ya jaddada bukatar gudanar da addu’o’i don dorewar zaman lafiya da inganta sha’anin tsaro.
A kokarinsa wajen inganta kiwon lafiya, Hon. Yusuf Dahiru Liman ya dauki nauyin mutane 200 da suka hada da tsofaffi da mabukata daga Kakuri-Gwari da unguwar Television domin shiga tsarin inshorar lafiya na KACHMA wanda ke ba da damar samun kulawar lafiya mai araha.
Baya ga hakan, Kakakin ya bayar da guraben karatu ga dalibai 200 daga wadannan al’ummomi domin tallafa musu a harkar ilimi da gina al’umma mai wayewa.
Bikin na Easter ya samu halartar shugabannin addini da sarakuna, shugabannin matasa da mata, da sauran manyan masu ruwa da tsaki na al’umma.
A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, Mr. James Kanyip ya yabawa nasarorin da aka samu wajen karfafa tsaro da inganta zaman tare a jihar. Ya bayyana cewa gwamnati na amfani da hanyoyin sasantawa da tattaunawa wajen magance matsalolin tsaro, tare da kira ga jama’a da su kasance masu lura da kuma sanar da hukumomi duk wani abin da ba su amince da shi ba.
Shugabannin al’umma su ma sun yi amfani da damar wajen yabawa Kakakin bisa kokarinsa na kawo ci gaba. Mista Monday Kazah daga Kakuri-Gwari da Mista Ishaya Amfani daga unguwar Television sun jinjinawa Hon. Liman saboda shirye-shiryensa na tallafawa jama’a ta hanyar bayar da guraben karatu, koyar da sana’o’i, da samar da ayyukan yi. Sun kuma tabbatar masa da goyon baya da addu’o’i domin samar da dokokin da za su bunkasa rayuwar jama’a.
Shamsuddeen Mannir Atiku
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
A wani yunkuri na inganta kula da mata masu juna biyu da sauran ayyukan kiwon lafiya a jihar Jigawa, Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF tare da hadin gwiwar Karamar Hukumar Kirikasamma sun mika kayayyakin aiki da wasu muhimman kayayyaki ga cibiyar kiwon lafiya ta farko a Kirikasamma.
Mai kula da cibiyar kiwon lafiya ta farko, Kabiru Musa, ya bayyana cewa kayayyakin sun haɗa da gadajen haihuwa, zannuwan gado, kayan aikin jinya, matashin kai da sauransu, kuma za a rarraba su zuwa wuraren kiwon lafiya a fadin karamar hukumar.
A cewarsa, kayan da UNICEF da karamar hukumar suka samar za su inganta yadda ake gudanar da ayyukan kiwon lafiya a yankin.
Yayin mika kayayyakin ga mai kula da cibiyar kiwon lafiya, shugaban karamar hukumar Kirikasamma, Alhaji Muhammad Maji Wakili Marma, ya bukaci ma’aikatan lafiya da su tabbatar da gaskiya da adalci a lokacin rabon kayan.
Haka kuma, ya yaba da kokarin Gwamna Umar Namadi da sauran abokan hulda wajen gyara cibiyoyin kiwon lafiya da gina gidajen Ungozoma a Kirikasamma da kuma fadin jihar domin inganta ayyukan kiwon lafiya.
Usman Muhammad Zaria