Leadership News Hausa:
2025-12-13@12:36:00 GMT

Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu

Published: 12th, April 2025 GMT

Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu

Ga kuma yadda ake sarrafawa:

Da farko, a zuba ruwa a tukunya a sa a wuta domin ya tafasa.

A rage wuta kadan, sannan a zuba garin alabo a hankali cikin ruwan da ke tafasa, ana juyawa da muciya ko cokali ko leda mai kauri don kada ya yi kolalla.

A ci gaba da juyawa har sai ya hade sosai kuma ya zama mai laushi.

Idan yana da kauri sosai, sai a kara dan ruwan zafi kadan wanda dama kin rage, kuma a ci gaba da juyawa har sai ya yi laushi.

A rufe shi na ‘yan mintuna kafin a sauke.

 

Sai kuma yadda ake miyar Uwedu:

Iata ma ga abubuwan da ake bukata domin hada ta:

Ganyen Ewedu (fresh leabes)

Kanwa ko potash (dan kadan),Gishiri, Magi, yaji

 

Sai kuma yadda ake hadawa:

A gyara ganyen Ewedu, a wanke su da kyau.

Sannan a zuba ruwa kadan a tukunya, a sa kanwa ko potash, a sa a tafasa.

Idan ruwan ya tafasa, sai a zuba ganyen uwedu, a dafa na kimanin minti 5–7. A sauke, sannan a daka a cikin turmi ko a murza da blender idan ana so ya zama ya yi laushi. Sai a mayar da shi tukunya, a sa gishiri da maggi da yaji idan ana so, a dafa na minti kadan sai a sauke.

A ci dadi lafiya.

Za’a dan iya zuba miyar ja ko nama ko ganda ko kifi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Miya Uwaidu

এছাড়াও পড়ুন:

Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa

Jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo.

Jam’iyyar ta tabbatar da rasuwar ce a cikin wata sanarwa da sakatarenta yada labaranta na kasa, Kwamared Ini Ememobong, ya fitar.

Rahotanni sun ce Ewhrudjakpo ya yanke jiki ya faɗi a ofishinsa da ke gidan gwamnati, Yenagoa, a ranar Alhamis, inda aka garzaya da shi zuwa Cibiyar Lafiya ta Ƙasa (FMC) da ke Yenagoa.

Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis.

An haifi Ewhrudjakpo ranar ranar biyar ga watan Satumban 1965, a ƙauyen Ofoni da ke Ƙaramar Hukumar Sagbama, Jihar Bayelsa. Ya rasu yana da shekaru 60.

Kodayake ba a san ainihin dalilin faɗuwarsa ba, majiyoyi sun ce ya faɗi ne ba zato ba tsammani yayin da yake gudanar da ayyukan ofis, lamarin da ya sa dogarai da ma’aikatansa suka yi gaggawar taimaka masa.

Wasu majiyoyi da ke kusa da marigayin sun nuna cewa mutuwarsa na iya zama sakamakon bugun zuciya.

Lamarin ya haifar da ɗan tashin hankali a gidan gwamnati da kuma fadin Yenagoa, inda mazauna garin suka nuna damuwa game da mutumin da suke kira da “Mataimakin Gwamna Mai Aikin Dare.”

Sun ce sau da yawa yana yin aiki har dare ba tare da hutu ba.

A lokacin da ake rubuta wannan rahoto da yammacin jiya, gwamnatin Jihar Bayelsa ba ta fitar da wata sanarwa ba a hukumance a kan lamarin.

Kazalika, da mai taimaka wa mataimakin gwamnan kan yaɗa labarai, Doubra Atazi, da kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Ebiuwou Koku-Obiyai, sun ƙi yin bayani lokacin da aka tuntube su.

Sai dai a cikin sanarwarta, PDP ta bayyana kaduwa da alhini kan rasuwar mataimakin gwamnan, tana bayyana shi a matsayin “amintaccen ɗan jam’iyya kuma mai gaskiya.”

Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar PDP ta kadu matuƙa da labarin rasuwar Mataimakin Gwamnan Jihar Bayelsa kuma ɗan jam’iyya mai aminci, Mai Girma Sanata Lawrence Oborawharievwo Ewhrudjakpo, wanda rahotanni suka ce ya faɗi ya rasu a yau.

“Wannan labari mai tayar da hankali ya jefa Kwamitin Zartarwa na Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki, SAN, da kuma dukkan mambobin jam’iyyarmu mai girma, musamman mambobinmu masu aminci a Jihar Bayelsa, cikin baƙin ciki mai yawa.

“Tun yana raye, Sanata Ewhrudjakpo ya kasance ɗan siyasa mai gaskiya da daidaito wanda ya yi siyasa bisa ƙa’ida. Mutum ne da ya yi tsayin daka, jagora ne wanda rayuwarsa ta ta’allaka da imani, gaskiya da ƙarfin hali. Ya tsaya tsayin daka kan waɗannan dabi’u har zuwa ƙarshe.

“Muna cikin baƙin ciki matuƙa da rasuwar wannan jarumin siyasa mai gaskiya, kuma muna roƙon Allah ya ba shi hutu na har abada. Muna mika ta’aziyyarmu ga gwamnati da al’ummar jihar Bayelsa kan wannan babban rashin da ba za a iya maye gurbinsa ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha