Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
Published: 10th, April 2025 GMT
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jagoranci wata tawaga zuwa Jihar Edo domin binciko gaskiyar abin da ya faru game da kisan mafarauta ’yan asalin jihar a ƙauyen Uromi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ne, ya umarci a kafa wannan tawaga, wacce ta ƙunshi manyan shugabanni irin su Sarkin Rano, Kwamishinonin ma’aikatu da kuma Shugaban Ƙaramar Hukumar Bunkure.
“Manufarmu a bayyane take – bincike, tattaunawa da bayar da shawarwari masu ɗorewa.
“Wannan ba kawai yawon neman gaskiya ba ne, har ila yau ƙoƙari ne na kawo zaman lafiya, domin hana sake faruwar irin wannan tashin hankali,” in ji mataimakin gwamnan
Tawagar za ta gana da Gwamnan Jihar Edo, hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin fararen hula domin fahimtar matsalar tare da kawo hanyoyin sasanci.
Gwarzo, ya ce tawagar za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin an samun zaman lafiya da hana faruwar irin wannan rikici a gaba.
Wannan ƙoƙari na cikin shirin Gwamnonin Arewa na haɗin kai da goyon bayan zaman lafiya a faɗin Najeriya sakamakon ƙaruwar rashin tsaro da ake fuskanta.
“Wannan shiri wani ɓangare ne na matakan haɗin gwiwar Gwamnonin Arewa domin nuna goyon baya, haɗin kai a ƙasa da kuma tunkarar matsalar tsaro da ke ƙaruwa a sassa daban-daban na Najeriya,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnatin Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo mafarauta mataimakin gwamna
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
An shawarci gwamnatocin jihohin Sakkwato, Kebbi da Zamfara da su kirkiro hanyoyi na wayar da kan al’umma dangane da shirye-shiryen tallafi da ayyukan ci gaba da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa domin bunkasa tattalin arziki da tabbatar da tsaro a yankunansu.
Shugaban sashen kimiyyar zamantakewa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Chika Umar Aliyu, ne ya bayar da wannan shawara yayin gabatar da takarda a wajen taron shekara-shekara na kungiyar Nigerian Institute of Management reshen jihar Sokoto na shekarar 2025, wanda aka hada da gabatar da lambar yabo ga wadanda suka cancanta.
Farfesa Chika ya bayyana cewa, gwamnati tarayya na da shirye-shiryen tallafi da dama da suka hada da na noma, kasuwanci da kuma koyar da sana’o’in hannu domin kara habaka tattalin arzikin ‘yan Najeriya da rage zaman kashe wando, da tayar da hankali musamman matasa a yankin.
Ya jaddada cewa dole ne gwamnatocin jihohi su tallafa wa kokarin gwamnatin tarayya ta hanyar amfani da hukumominsu na jin dadin al’umma domin cimma burin shirye-shiryen.
A jawabinsa wajen taron, kwamishinan noma na jihar Sakkwato, Muhammad Tukur Alkali, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta sayo manyan Tan-tan na noma guda 250 da kayan aikin gona da darajarsu ta kai naira biliyan ashirin da biyu da miliyan dari daya (₦22.1bn), domin tabbatar da wadatar abinci.
A cewar Tukur Alkali, gwamnatin jihar ta hanyar shirye-shiryen inganta rayuwar al’umma, ta samar da sama da ayyukan yi 2,700 a bangaren noma, abin da ke da tasiri mai girma wajen bunkasa noma mai dorewa da ci gaban ababen more rayuwa a karkara.
Daga Nasir Malali