Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
Published: 10th, April 2025 GMT
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jagoranci wata tawaga zuwa Jihar Edo domin binciko gaskiyar abin da ya faru game da kisan mafarauta ’yan asalin jihar a ƙauyen Uromi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ne, ya umarci a kafa wannan tawaga, wacce ta ƙunshi manyan shugabanni irin su Sarkin Rano, Kwamishinonin ma’aikatu da kuma Shugaban Ƙaramar Hukumar Bunkure.
“Manufarmu a bayyane take – bincike, tattaunawa da bayar da shawarwari masu ɗorewa.
“Wannan ba kawai yawon neman gaskiya ba ne, har ila yau ƙoƙari ne na kawo zaman lafiya, domin hana sake faruwar irin wannan tashin hankali,” in ji mataimakin gwamnan
Tawagar za ta gana da Gwamnan Jihar Edo, hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin fararen hula domin fahimtar matsalar tare da kawo hanyoyin sasanci.
Gwarzo, ya ce tawagar za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin an samun zaman lafiya da hana faruwar irin wannan rikici a gaba.
Wannan ƙoƙari na cikin shirin Gwamnonin Arewa na haɗin kai da goyon bayan zaman lafiya a faɗin Najeriya sakamakon ƙaruwar rashin tsaro da ake fuskanta.
“Wannan shiri wani ɓangare ne na matakan haɗin gwiwar Gwamnonin Arewa domin nuna goyon baya, haɗin kai a ƙasa da kuma tunkarar matsalar tsaro da ke ƙaruwa a sassa daban-daban na Najeriya,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnatin Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo mafarauta mataimakin gwamna
এছাড়াও পড়ুন:
Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
Wani bon kirar hannu da aka dasa akan hanyar dake hada Rann da Gamboru a jihar Borno ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 6.
Daga cikin wadanda su ka rasa rayukansu sanadiyyar tashin bom din sun hada mata da kananan yara kamar yadda majiyar ‘yan sanda ta sanar.
Kungiyar nan mai suna; gwamnatin musulunci a yammacin Afirka ce ta sanar da daukar alhakin kai hari na ranar Litinin din da ta gabata.
Bugu da kari sauran wadanda su ka rasa rayukan nasu manoma ne da suke cikin motar a-kori-kura da ta taka nakiya.
Baya ga wadanda su ka rasa rayukansu, wasu mutanen su 3 sun jikkata,kuma tuni an dauke su zuwa asibiti domin yi musu magani.
Wani dan sintiri da yake aiki da rundunar fararen hula masu taimakawa jami’an tsaro, Abba Madu, ya shaida wa manema labaru cewa; Da alamu an dasa bom din domin ya tashi da jami’an tsaro da suke yin sintiri akan wannan hanyar.
Kungiyoyin ‘yan ta’adda sun saba dasa irin wadannan nakiyoyin da bama-baman akan hanyar da jami’an tsaro suke bi.
Kungiyar nan da take kiran kanta; Gwamnatin Musulunci a yammacin Afirka wacce a takaice ake kira; “ISWAP” ce ta dauki nauyin kai harin.
Tun a 2009 ne yankin Arewa maso gabashin kasar ta Najeriya yake fama da matsalar kungiyoyi masu dauke da makamai da su ka hada Bokoharam, sannan kuma daga baya waje 2016, kungiyar gwamnatin musulunci a yammacin Afirka.