Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya
Published: 28th, March 2025 GMT
kungiyar ta koka kan cewa bai dace a yi amfani da EFCC wajen kamun Jami’an gwamnatin jihar Bauchi da nufin nuna yatsa wa Gwamna Bala Muhammad wanda ya kasance mai fitowa da hakikanin gaskiyar halin da talakawa ke ciki da nema musu hakkinsu daga wajen shugaban kasa.
kungiyar ta lura da cewa in ana amfani da irin wannan salon lallai za a samu nakasu wajen kyautata demukradiyya a kasar nan domin mutane da dama za su yi shiru kan abubuwan da suke tafiya ba daidai ba domin gudun musgunawa.
Eyes on Democracy ta kuma nuna shakku kan yadda aka kama Akanta Janar din a lokacin da yake halartar taron FAAC a Abuja, inda ta bayyana cewa hukumar EFCC ba ta gayyace shi ba balle ya ki zuwa da har za a dauki matakin kamashi.
“Babu ko shakka cewa Gwamna Bala Mohammed yana tafiyar da harkokin kudi da dukiyar jihar cikin tsanake da gaskiya, a karkashin shugabancinsa jihar Bauchi na samun ci gaba da ba a tava ganin irinsa ba kuma cikin sauri a sassa daban-daban,” kungiyar ta shaida.
Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Nijeriya, kungiyoyin farar hula, da sauran kasashen duniya da su lura da wadannan ayyukan da ba su dace da tsarin dimokradiyya ba, su bijirewa duk wani yunkuri na mayar da hukumar EFCC dandalin cin zalin siyasa.
Bugu da kari, kungiyar ta yi kira ga hukumar EFCC da ta yi aiki bisa doka, sannan ta bukaci da a gaggauta sakin Akanta Janar din, idan har akwai zarge-zarge na gaskiya da ake yi masa, kungiyar ta dage cewa a bi su kamar yadda doka ta tanada.
“Muna tsayawa tsayin daka da Gwamna Bala Mohammed da dukkan masu fada a ji na gaskiya da adalci a Nijeriya. Babu wata barazana da za ta hana a gudanar da gangamkn na tabbatar da dimokuradiyya, gaskiya da rikon amana,” in ji ƙungiyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kungiyar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Mista Mark Joseph Carney murna bisa zaɓensa a matsayin Firaiminista na 24 na ƙasar Kanada, bayan nasarar jam’iyyar Liberal a zaɓen majalisar dokokin da aka kammala kwanan nan.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana zaman Carney a wannan matsayi a matsayin wani muhimmin ci gaba, musamman a wannan lokaci da Kanada ke bukatar gogaggen shugaba domin fuskantar ƙalubale da dama.
Carney, wanda fitaccen masani ne a fannin tattalin arziki, ya taba rike mukamin Gwamnan Babban Bankin Kanada daga shekarar 2008 zuwa 2013, sannan ya ci gaba da zama Gwamnan Babban Bankin Ingila daga 2013 zuwa 2020.
Shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwar cewa ƙwarewar sabon shugaban Kanada a fannin kuɗi da shugabanci za ta taka muhimmiyar rawa wajen gina makomar ƙasar. Haka kuma, ya sake jaddada kudirin Najeriya na ƙarfafa dangantakar diflomasiyya da Kanada, musamman a fannonin ilimi, sauyin yanayi da hijira.
Shugaban Najeriya ya ƙara da cewa yana fatan kafa kyakkyawan hadin gwiwa da gwamnatin Carney, yayin da ya nuna godiyarsa ga kyakkyawar alakar da aka kula a tsakaninsu a zamanin tsohon Firayim Minista, Justin Trudeau.
Bello Wakili