Aminiya:
2025-06-15@13:15:19 GMT

’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa

Published: 26th, March 2025 GMT

Wasu mutane huɗu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun mutu a sakamakon hatsarin mota a Jihar Nasarawa.

Kakakin rundunar ‘yan sanda jihar SP Nansel Rahman, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce lamarin ya auku ne lokacin da ‘yan fashin ke ƙoƙarin tserewa jami’an.

Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati

“A ranar 25 ga watan Maris ne rundunarmu ta samu wani kiran gaggawa kan wasu ‘yan fashi na tsaka da ta’asa a bayan filin wasa na ƙaramar hukumar Keffi.

“Bayan samun kiran ne kwamishinan ‘yan sanda Shettima Jauro Mohammed ya ba da umarnin bin bayan ‘yan fashin nan take.

“Suna cikin guje mana ne a cikin motar da suka sace ƙirar Toyota Camry suka yi haɗari a babban titin Abuja-Keffi.

“Jami’anmu da ke ofishin ‘yan sanda na Goshen ne suka kwashe su zuwa asibiti, a nan mutum huɗu suka mutu.

“Ɗayan da ya rage kuma na hannunmu likitoci na bashi kulawa.

Binciken ‘yan sanda dai ya kai ga gano wasu kayan da ‘yan fashin suka sata da suka haɗa wayoyin hannu 12, agogunan hannu, sai makamai da suka haɗa da manyan wuƙaƙe biyu, sukundireba, da kuma layu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nasarawa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran

Isra’ila ta kaddamar da hare hare kan wasu gine-gine da cibiyoyi a sassa daban daban na Iran ciki har da Tehran babban birni a cikin daren jiya wayewar wannan safiya ta Juma’a.

Kafofin yada labarai na Iran sun ce akwai mata da yara da dama daga cikin wadanda suka yi shahada a hare-haren.

An kuma bayar da rahoton kai hari a wurare a Natanz, Khorramabad, da Khondab, da dai sauransu.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin da Isra’ila ta kai wa Iran zai kai tsawon kwanaki idab akwai bukatar hakan.

“Za a ci gaba da gudanar da wannan aiki na tsawon kwanaki kamar yadda ake tsara don kawar da wannan barazanar,” in ji Netanyahu a cikin wata sanarwa ta bidiyo.

Hare-haren da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai kan Tehran ya yi sanadiyar shahadar wasu fitattun masana kimiyyar nukiliya na Iran, Mohammad Mahdi Tehranchi da Fereydoon Abbasi, dama wasu fararen hula.

Tehranchi shi ne shugaban jami’ar Azad ta Musulunci ta Iran.

Fereydoon Abbasi ya kasance tsohon shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran.

An dakatar da zirga-zirgar jiragai a filin jirgin saman Imam Khumaini na Tehran.

Harin ya zo ne kwanaki biyu gabanin wani sabon zagaye na shawarwarin nukiliyar Iran da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara