’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa
Published: 26th, March 2025 GMT
Wasu mutane huɗu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun mutu a sakamakon hatsarin mota a Jihar Nasarawa.
Kakakin rundunar ‘yan sanda jihar SP Nansel Rahman, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce lamarin ya auku ne lokacin da ‘yan fashin ke ƙoƙarin tserewa jami’an.
Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati“A ranar 25 ga watan Maris ne rundunarmu ta samu wani kiran gaggawa kan wasu ‘yan fashi na tsaka da ta’asa a bayan filin wasa na ƙaramar hukumar Keffi.
“Bayan samun kiran ne kwamishinan ‘yan sanda Shettima Jauro Mohammed ya ba da umarnin bin bayan ‘yan fashin nan take.
“Suna cikin guje mana ne a cikin motar da suka sace ƙirar Toyota Camry suka yi haɗari a babban titin Abuja-Keffi.
“Jami’anmu da ke ofishin ‘yan sanda na Goshen ne suka kwashe su zuwa asibiti, a nan mutum huɗu suka mutu.
“Ɗayan da ya rage kuma na hannunmu likitoci na bashi kulawa.
Binciken ‘yan sanda dai ya kai ga gano wasu kayan da ‘yan fashin suka sata da suka haɗa wayoyin hannu 12, agogunan hannu, sai makamai da suka haɗa da manyan wuƙaƙe biyu, sukundireba, da kuma layu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kissoshin Kayuwa: Sirar Imam Hassan(a) 122
122- Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da haka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtadha Muttahhari, ko kuma cikin littafin mathnawa na maulana Jalaluddeen Rum ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.
////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata a kuma cikin sarir Imam Al-Hassan Almujtaba (a) diyar Fatima (s) kuma jikan manzon All..(s) na farko, idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun bayyana yadda.
Ummul muminina Aisha matar manzon All..(s) ta gabatar da khuba mai tsawo a Makka tana kirin mutanen Birnin su fito tare da ita cewa, Basra na kasar Iraki don neman jinin Khalifa Uthman, sannan daga cikin wadanda suka kira har da sauran ummahatul muminin, daga cikin har da umma salama. Inda ta shiga tana yabunta, daga karshe Ummu Salma (r ) ta yi mata nasiha, ta kuma tunanatar da ita girman Aliyu dan Abitalib (a) a wajen manzon All..(a), amma bata dauka ba. Sannan ta kama hanyarta zuwa Madina, ta kuma rubutawa Amirul muminina (a) wasika inda ta fada mata Shirin Aisha. Sannan ta aiki danta da wasikar ta bukaci danta Umar dan Abisalma ya taimaka masa a kan makiyansa.
Har’ila yau malaman tarihi sun bayyana cewa Yaala dan Umayya dan Ubaidata Attamini. Wanda ya kasance walin Khalifa Umar a wasu wurare a kasar Yemen, sannan Khalifa Uthman ya sanyashi wali a birnin Sanaa abban birnin kasar Yemen. Sannan daga karshe ya ji labarin kissan Khalifa Uthman yana babban kwamandan sojojin a kasar Yemen.
Don haka ya yi sauri don ya taimaka masa, amma kafin ya iso madina ya ji an kasashe. A lokacinda ya zo Makka ya ji abinda Aisha da Talha da Zubair suke kokarin yi, sai ya taimaka masu. Ya bawa Zubair dinari dubu 400. Sannan ya bawa sojojin Aisha 70 guzurin hanya don zuwa tare da ita. Banda haka ance shi ya bawa Aisha rakumin da ta hau wacce ake kiranta Askar.
Don haka a lokacinda Aisha ta fita daga makka, ta yi tafiya da rundunarta har tayi zango a wani wuri da ake kira Zeekar kusa da kufa. Sai ta hadu da Sa’eed dan Ass daya daga cikin gwamnonin Usman a Kufa, bayan walid.
Sai saeed Al-umawi ya tambayeta: Ina zaki je ya Ummul muminin? Sai tace: Basra,
-Me zaki yi a can.
-Ina neman fansar jinin Uthman.
Sai yayi Dariya, snnan yace: Ga wadannan tare da ke su suka kashe Uthman, sai ta juya fuskanta daga gare shi. Daga nan sai ya wuceta, ya ji wajen Marwan ya ce masa: Kaima kana zuwa basra ne ? sai yace : ee.
-Me kake so?
– Ina neman fansar jinin Khalifa Uthman.
-To ai ga wadanda suka kashe Uthman tare da kai. Wannan mutane biyu sune suka kashe Uthman, suna sun khalifanci wa kansu, A lokacinda ta fice daga hannunsu. Sai suka ce: Zamu wanke jinni da jinni. Laifi da tuba. Bai saurare shi ba. Sun ci gaba a kan hanyarsu ta zaluntar Amirul muminina da kuma raba kan al-ummar manzon All..(s) kan karya.
A cikin tafiyarsu zuwa Basra sai dare ta riskesu a wani wuri da ake kira Haw’abu, akwai ruwa a wurin, sai taji karnuka suna haushin ayarinta, sai ta tsorata. Sai ta kira Muhammad dan Talha dai Ubaidullahi, ta tambaye shi. Wani ruwa ne wannan sai yace: Haw’abu.
Sai kara tsorata, sannan da yi nadamar abinda ya fito da ita. Sai ce: Ai ni zan koma!
-me yasa?
-Naji manzon All…(s) yana fadawa matansa: Kamar ina ganin daya daga cikinku hakika karnukan Haw’aba sun yi mata haushiu, kuma ina maki gargadi kada ki kasance ita, ya ke humaira.
Sai Muhammad dan Talha yace mata: Ki bar wannan maganar, mu wuce. Amma ba ta gamsu da maganarsa ba. Ta dage kan cewa zata juya ta koma. Ana cikin wannan halin sai labari ya kaiwa Talha da Zubair wanda suke cikin ayarinta. Sai suka taho wakinta, sun yi mata Magana, amma bata gamsu ba.
Sun kuma tabbatar da cewa idan ta fice daga cikinsu to abinda suke fatan samu ya tafi a banza.
Don haka sai suka kawo mata mutane, wadanda suke saye su, wasu suka ce yawansu ya kai 50, suka rantse da All..kan cewa wannan wurin ko wannan Ruwan ba Ruwan Haw’aba bane. Ance wannan shi ne shaidar Zur na farko a musulunci.
Da abinda ya dace mata, shi ne ta koma gidanta, bayan ta tuna da hadisin mikinta manzon All…(s). Amma sai ta gamsu da karyan da wasu suka yi mata, sai ta ce gaba ta je ta jawo raba kan al-ummar musulmi tare da yakar dan uwan manzon All..(s).
A lokacinda suka isa kusa da garin Basra. Suka yi sansani a wajen garin. Sai gwamnan garin Basra a lokacin shi ne, Uthman bin Hunaifa mutumin Madina ne daga kabilar Aws.
Kafin Imam Ali (a) ya nada shi walin Basra, ya taba zama gwamnan garin a lokacin Khalifa Umar, ya kuma yi aiki mai kyau na kyautata ayyukan numa. Sannan a lokacinda Imam Ali ya nemi shawarar mashawartansa suka nuna masa shi sai ya sake tura shi gwamnan Basra.
Don haka sai Uthman bin Hunaifa, ya aiki Abu aswad Addu’ali zuwa wajenta, don sanin abinda ya zo da ita.
A lokacinda Abul Aswad Addua’ly ya isa wajenta sai yace mata: Me yazo da key a ummul muminina ko?
Sai tace: Neman jikin Uthmanu.
-babu mutun ko daya, a Basra daga cikin wadanda suka kashe uthman.
-Ka yi gaskiya, amma kuna tare da Aliyu dan Abitalib (a) dake Madina. Na zo don kiran mutanen Basra saboda yakarsa. Ba za muyi fushi da ku kan faduwar Uthman ba, amma ba zamu yi fushi wa Uthman daga takubbanku ba.?
Sai Abu Aswad Addu’ali ya mayar mata da kalmomi masu hikima. Yana cewa: Me ya hadaki da bulala da kuma takobi? Ai abinda muka sani ke masoyiyar manzon All..(s). ya umurceki ki zauna a gidanki, ki karanta littafin Ubangijinki, yaki bai wajaba a kan mata ba. Kuma ba ruwansu da neman jinin wanda aka kashe.
Kuma lalle Aliyu ya fi cancanta da ke, kuma ya fi ki kusa da shi a kan wannan al-amarin. Don dukkanku yan abdul manaf ne.
Sai tace: Ba zan je ko ina ba, sai na yi abinda ya kawo ni. Shin Abu aswad kana tsammanin wani ya isa ya yake ni? Sai yace mata: Na rantse da All..Za’a yake ki, yaki mai tsanani.
Sannan ya barta, yaje wajen Zubaira, sai ya tunatar da shi, abinda ua shude na biyayyarsa ga Aliyu dan Abitalib (a). Yana cewa: Ya Baban Abdullahi, mutane sun sanka da cewa, a ranar da aka yi bai’a wa Abubakar, kana rike da takobinka kana cewa: ba wanda ya cancanci wannan al-amarin in banda dan Abitalib(a), ina wannad matsayin da wannan.
Sai Zubair yace: Muna neman Jinin Uthman.
-Kai da abokinka, kun yi masa bai’a kamar yadda na sami labari. Sai Zubair ya karaya, da nasihan Abu Aswad Addu’ali ya yi masa, ya tabbatar da cewa shi ne gaskiya da shiriya. Sai yacewa Abu Aswad ya je yayi magana da abokinsa Talha dan Ubaidullah ikan al-amarin.
Sai Abuaswad Addu’ali ya je yayiwa Talha dan ubaidullahi Magana, amma ya dage kan cewa, sai sun yaki Amirulmuminina (a).
Sai Abu Aswad ya koma wajen Uthman dan Hunaif ya fada masa abinda ya ji ya gana daga wadannan mutane, da kuma dagewarsu sai sun yaki Ali (a) da kuma magoya bayansa.
Daga nan sai dan Hunaif ya tare mutanen Basra yayi masu khuduba yana cewa: Ya ku mutane! Abin sani kawai shi ne kun yi mubaya’a ga All..
{Hannun All..yana kan hannayensu, wanda ya kunce , to lalle hakiki ya kwancewa kansa, wanda kuma ya cika abinda yayiwa All..alkawali, to da sannu zai bashi lada babba}
Na rantse da All…da Aliyu ya san cewa akwai wanda ya cancanci wannan al-amarin da bai karbe shi ba. Da kuma mutane sun yi bai’a ga wani da yayi masa mabaya’a kuma ya yi biyayya a gareshi. Baya bukatar wani daga sahabban manzon All..(s). amma ba wani daga cikinsu wanda baya bukatar taimakonsa.
Kuma hakika ya yi tarayya da su a kyawawansu, ba wanda yayi tarayyar da shi a kyawansa.
Wadan nan mutane biyu -wato Talha da Zubair-sun yi masa mubaya, ba All.. suke nufi ba da wannan fitarsu ba. Sai dai sun gaggauta yaye ne kafin lokacinsa shayarwa ya kare, sanna sun gaggauta shayarwa kafin haihuwa. Haka ma haihuwa kafin daukar ciki.
Sun nemi ladar All..daga bayinsa. Sun riya cewa sun yi bai’a a dole, — har zuwa inda yake cewa. Ku saurara, gaskiya tana tare da mutane gama gari, kuma mutane suna kan bai’ar Aliyu. Me kuke gani yak u mutane?
Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalamu alaikum wa rhamatullahi wa barakatuhu.