Aminiya:
2025-06-15@14:35:00 GMT

Ban taɓa fuskantar tsangwama a Kannywood ba — Prince Aboki

Published: 26th, March 2025 GMT

Daraktan Fim ɗin Mai martaba, Prince Daniel (ABOKI), ya ce ba gaskiya ba ne batun da ake yaɗawa cewa yana fuskantar tsangwama a Kannywwod saboda bambancin addininsa.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Aboki ya ce shi ma batun cewa ana nuna masa bambamci a Nollywood saboda ɗan arewa ne ba shi da tushe balle makama.

Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku

“Wasu labarai da aka wallafa na nuna cewa wai masana’antar Kannywood ta ƙi amincewa da ni saboda addini na, ita kuma Nollywood saboda ni ɗan Arewa ne.

“Da farko dai ban yi hira da wata jarida ko kafar yaɗa labarai ba dangane da wannan batu. Amma duk da haka bari na ɗan yi ƙarin haske.

“Na halarci wani taron masana’antar Nollywood da Hollywood a birnin Los Angeles na Jihar California da ke Amurka a farkon wannan watan, inda a sashen tambaya da amsa na taron aka tambaye ni ƙalubalen da muka fuskanta lokacin fim ɗin Mai Martaba da gwagwarmayar da muka yi kafin kai wa matakin kambun fina-finan duniya na Oscar.

“Na faɗi abubuwa da dama da suka haɗa da fargabar matsalar tsaro da na masu ɗaukar nauyi kasancewar babu wanda yake son yin kasadar ba mu kuɗinsa, la’akari da cewa ni sabon darakta ne wanda ke aiki tare da sababbin jarumai.

“A wani lokacin ɓangaren masana’antar Kannywood na yi mana kallon ‘yan Nollywood, su ma Nollywood suna kallonmu a matsayin ‘yan Kannywood, saboda kawai ni ɗan Arewa ne.

“Na yi wannan bayanin ne da kyakkyawar niyya domin taimaka wa masu sauraro a cikin zauren su fahimci ɓangarorin masana’antar Fina-finai a Najeriya da kuma yadda yake da ƙalubale a gare mu a lokacin.

“Domin fayyace zahiri, masana’antar Kannywood ba ta taɓa nuna min ƙiyayya ba ta ƙabilanci ko addini.

“Hasalima, masana’antar ce babban ginshiƙin goyon bayan da na samu a matsayina na mai shirya fim.

“An nuna min ƙauna a fili ta hanyar babban goyon bayan da muka samu daga masu kallo da sauran al-umma a lokacin da muka nuna fina-finanmu a gidajen kallo, da kuma ƙarfafawa daga ƙwararrun ‘yan masana’antar tsofaffi da sababbin shiga,” in ji shi.

Fim ɗin Mai martaba dai an haska shi ne kimanin watanni takwas da suka gabata, kuma ci gaba ne kan wasan kwaikwayon gidan Rediyon Arewa da ke Kano mai taken ‘Kasar Jallaba”, inda Prince aboki ke aiki a matsayin jagoran sashin shirye-shirye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kannywood masana antar

এছাড়াও পড়ুন:

Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano

Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daba masa wuta.

Bayanai sun nuna cewa barayin sun ritsa shi ne a yankin unguwar Sheka da ke karamar hukumar Kumbotso, inda suka sossoke shi da wuka a ciki kuma suka kwace wayarsa, a ranar Laraba.

BBC ya ruwaito mutumin ya rasu bayan da aka garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, a ranar Juma’a.

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jami’ar (NASU), Kwamared Bashir Muhammad, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya yi kira ga gwamnatin Jihar Kano da sauran hukumomi da su ɗauki tsattsauran mataki a kan kisan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka