Aminiya:
2025-09-17@21:51:43 GMT

Ban taɓa fuskantar tsangwama a Kannywood ba — Prince Aboki

Published: 26th, March 2025 GMT

Daraktan Fim ɗin Mai martaba, Prince Daniel (ABOKI), ya ce ba gaskiya ba ne batun da ake yaɗawa cewa yana fuskantar tsangwama a Kannywwod saboda bambancin addininsa.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Aboki ya ce shi ma batun cewa ana nuna masa bambamci a Nollywood saboda ɗan arewa ne ba shi da tushe balle makama.

Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku

“Wasu labarai da aka wallafa na nuna cewa wai masana’antar Kannywood ta ƙi amincewa da ni saboda addini na, ita kuma Nollywood saboda ni ɗan Arewa ne.

“Da farko dai ban yi hira da wata jarida ko kafar yaɗa labarai ba dangane da wannan batu. Amma duk da haka bari na ɗan yi ƙarin haske.

“Na halarci wani taron masana’antar Nollywood da Hollywood a birnin Los Angeles na Jihar California da ke Amurka a farkon wannan watan, inda a sashen tambaya da amsa na taron aka tambaye ni ƙalubalen da muka fuskanta lokacin fim ɗin Mai Martaba da gwagwarmayar da muka yi kafin kai wa matakin kambun fina-finan duniya na Oscar.

“Na faɗi abubuwa da dama da suka haɗa da fargabar matsalar tsaro da na masu ɗaukar nauyi kasancewar babu wanda yake son yin kasadar ba mu kuɗinsa, la’akari da cewa ni sabon darakta ne wanda ke aiki tare da sababbin jarumai.

“A wani lokacin ɓangaren masana’antar Kannywood na yi mana kallon ‘yan Nollywood, su ma Nollywood suna kallonmu a matsayin ‘yan Kannywood, saboda kawai ni ɗan Arewa ne.

“Na yi wannan bayanin ne da kyakkyawar niyya domin taimaka wa masu sauraro a cikin zauren su fahimci ɓangarorin masana’antar Fina-finai a Najeriya da kuma yadda yake da ƙalubale a gare mu a lokacin.

“Domin fayyace zahiri, masana’antar Kannywood ba ta taɓa nuna min ƙiyayya ba ta ƙabilanci ko addini.

“Hasalima, masana’antar ce babban ginshiƙin goyon bayan da na samu a matsayina na mai shirya fim.

“An nuna min ƙauna a fili ta hanyar babban goyon bayan da muka samu daga masu kallo da sauran al-umma a lokacin da muka nuna fina-finanmu a gidajen kallo, da kuma ƙarfafawa daga ƙwararrun ‘yan masana’antar tsofaffi da sababbin shiga,” in ji shi.

Fim ɗin Mai martaba dai an haska shi ne kimanin watanni takwas da suka gabata, kuma ci gaba ne kan wasan kwaikwayon gidan Rediyon Arewa da ke Kano mai taken ‘Kasar Jallaba”, inda Prince aboki ke aiki a matsayin jagoran sashin shirye-shirye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kannywood masana antar

এছাড়াও পড়ুন:

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce alkaluman baya bayan nan da aka fitar cikin Mujallar Economist, sun shaida yadda hada-hadar cinikayyar fitar da hajoji ta kasar Sin ke kara bunkasa cikin sauri a shekarar nan ta bana, inda fannin ke samun karuwar abokan hulda, da daidaiton matsayi cikin tsarin samar da hajojin masana’antu na kasa da kasa.

Kakakin ya kara da cewa, kasashen duniya suna maraba da hajojin kasar Sin, kuma yakin ciniki da haraji ba su yi wani babban tasiri kan kasar Sin ba. A fannin hada-hadar cinikayya, sanya shinge ba alama ce ta karfin gwiwa ba, kuma katangar da Amurka ke ginawa kanta, daga karshe za ta illata karfinta ne.

Lin Jian, wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa a yau Laraba, ya ce yayin da ake fama da yanayi mai sarkakiya, da sauye-sauye masu maimaituwa daga ketare, cinikayyar waje ta Sin na gudana lami lafiya, cike da karfin juriya da babban karsashi.

Hakan a cewarsa, ya shaida gazawar yakin haraji da cinikayya wajen girgiza fifikon da Sin ke da shi, a fannin raya masana’antun sarrafa hajoji da kasar ta gina a tsawon lokaci. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta