EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi
Published: 23rd, March 2025 GMT
Jami’an Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC) na shiyyar Gombe, sun kama wasu mutane 21 da ake zargi da damfarar Intanet a Jihar Bauchi.
A cewar wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook a ranar Litinin, “An kama wadanda ake zargin ne ta hanyar samun sahihan bayanan sirri kan zargin da ake yi musu na damfarar Intanet a yankin Kaure New Government Reservation Area, Bauchi da Awala, a titin Maiduguri, Jihar Bauchi.
“Abubuwan da aka kwato daga hannunsu a wajen kama su sun hada da motoci kirar BMW daya da Toyota Camry, PlayStation 5 guda uku, wayoyi masu tsada 30, da babbar talabijin daya, injin PoS guda shida, iPad guda hudu, da kwamfyutoci biyar.”
Sanarwar ta ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
Ya ce, “Muna matukar godiya ga gwamnatin Amurka saboda dorewar kawancen dabarun hadin gwiwa da Nijeriya.”
Ya kara da cewa, sayan jirage masu saukar ungulu na AH-1Z Viper zai kara inganta yakin da NAF ke yi, da kwazon aiki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp