Kasashen larabawa sun yi kakkausar suka ga matakin da Isra’ila ta dauka na dakatar da shigar da duk wani kayan agaji a zirin Gaza, suna masu bayyana hakan a matsayin keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas da kuma dokokin kasa da kasa.

Ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya a cikin wata sanarwa ta ce “Masar ta yi Allah-wadai da kuma yin tir da matakin da gwamnatin Isra’ila ta dauka na dakatar da agajin jin kai ga Gaza, tare da yin amfani da shi a matsayin wani makami na cin zarafi da azabtarwa.

Masar ta kuma yi Allah wadai da matakin da Isra’ila ta dauka na hana shigar da duk wani agajin jin kai a zirin Gaza a matsayin “ketare iyaka” na yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.

Ma’aikatar harkokin wajen Masar a cikin wata sanarwa da ta fitar “ta yi kakkausar suka ga matakin da Isra’ila ta dauka na hana agajin jin kai da mashigin da ake amfani da shi wajen kai agaji.”

Ma’aikatar ta ce “wadannan ayyukan sun saba wa yarjejeniyar tsagaita bude wuta, dokar jin kai ta kasa da kasa, Yarjejeniyar Geneva ta Hudu, da dukkan ka’idojin addini.”

Yarjejeniyar Geneva ta hudu da aka amince da ita a shekarar 1949 bayan yakin duniya na biyu, ta ta’allaka ne kan ba da kariya ga fararen hula, ciki har da yankunan da aka mamaye.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta dauka na

এছাড়াও পড়ুন:

An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna

Wata ’yar kasuwa mai taimakon al’umma, Barista Catherine Bitrus, ta raba wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a garin Manchok da ke Ƙaramar Hukumar Kaura, a Jihar Kaduna.

Tallafin ya haɗa da injinan niƙa, buhunan shinkafa, katan-katan na taliyar yara, da man girki.

Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima

A lokacin rabon kayan, Catherine, shugabar kamfanin Natural Beauty Secret, ta ce ta yi hakan ne domin taimaka wa matan karkara da ke fama da matsaloli a rayuwa.

“Allah Ya ba ni arziƙi, shi ya sa na ga dacewa na raba da waɗanda ke bukata,” in ji ta.

“Na zaɓi mata ne domin na san irin wahalar da suke sha.”

Ta roƙi matan da su dage da ƙoƙari, ka da su yanke ƙauna, domin komai na duniya yana da mafita idan aka jajirce.

Catherine ta ce tana da niyyar ci gaba da wannan aiki, kuma ta yaba wa Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, saboda irin goyon bayan da yake bai wa mata a jihar.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Barista James Kanyip, ya yaba da wannan aiki, inda ya buƙaci sauran masu hali da ƙungiyoyin su dinga tallafa wa marasa ƙarfi.

Shugaban kwamitin shirya taron, Lucky Ezra, ya bayyana Catherine a matsayin mace mai zuciyar taimako da kishin jama’a.

A madadin sauran matan da suka amfana, Josephine Bature ta nuna farin ciki da godiya, tare da addu’ar Allah Ya saka wa Catherine da alheri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje