HausaTv:
2025-06-15@07:47:20 GMT

MDD, Ta Damu Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji Gaza

Published: 3rd, March 2025 GMT

Babban jami’in bada agaji na Majalisar Dinkin Duniya ya kira matakin da Isra’ila ta dauka na dakatar da agajin dake shiga Gaza a matsayin abin damuwa.

Jami’in bayar da agajin gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher, ya yi kakkausar suka ga matakin da Isra’ila ta dauka na katse taimakon da take baiwa Gaza, yana mai cewa abin takaici ne.

A wani sako da ya wallafa a shafukan sada zumunta, ya tuna cewa “Dokar kasa da kasa ta bayyana karara cewa dole ne a bar agajin jin kai ya shiga zirin Gaza.”

Hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da dama da kwararru kan kare hakkin bil adama sun yi gargadin cewa wannan mataki ya zama keta dokokin kasa da kasa da kuma tauye hakkin bil’adama.

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Norway (NRC) ta jaddada cewa dakatar da tallafin da Isra’ila ke yi gaba daya zai haifar da mummunan sakamako ga fararen hula fiye da miliyan biyu da tuni ke fuskantar yunwa.

“Taimakon jin kai ba gata ba ne, hakki ne,” in ji Angelita Caredda, darektan yankin NRC na Gabas ta Tsakiya da Arewacin Afirka.

A halin da ake ciki, kungiyar likitoci marar iyaka (MSF) ta yi kakkausar suka ga Isra’ila saboda amfani da agajin jin kai a matsayin makami.

“Bai kamata a yi amfani da taimakon jin kai a matsayin makamin yaki ba,” in ji kungiyar agaji ta likitoci ta kasa da kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

Ya kuma tuna irin muhimmiyar rawar da Majalisar tarayya ta taka a lokuta masu sarƙaƙiya a tarihin Nijeriya, ciki har da daƙile shirin ƙara wa’adi na uku da kuma kafa “Dokar Bukata” lokacin rasuwar tsohon shugaban ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • IRGC : Iran a shirye take na tunkarar duk wani yanayi
  • Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe