HausaTv:
2025-09-18@00:39:16 GMT

Masar : Za’a Gabatar Da Shirin Baiwa Falasdinawa Yancin Zama A Kasarsu

Published: 3rd, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Masar Badr Abdelatty ya ce shirin sake gina Gaza wanda ya baiwa Falasdinawa yancin ci gaba da zama a kasarsu, za a gabatar da shi a taron gaggawa na kasashen Larabawa da za a yi a wannan mako.

Abdelatty a wani taron manema labarai a ranar Lahadin nan ya jaddada cewa shirin sake gina ba zai kasance na Masar ne kawai ko kuma na Larabawa ba amma zai nemi goyon bayan kasa da kasa don tabbatar da aiwatar da shi cikin nasara.

Abdelatty ya ce “Za mu yi tattaunawa mai zurfi tare da manyan kasashe masu ba da taimako da zarar an amince da shirin a taron kasashen Larabawa mai zuwa.”

Abdelatty ya ce bayan taron gaggawa na kasashen Larabawa da za a yi a ranar 4 ga Maris, za a yi taron ministocin kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC cikin gaggawa, inda ministocin harkokin wajen kasashen waje za su matsa kaimi wajen gabatar da sakamakon taron a duniya.

Abdelatty ya kara da cewa “Za mu tabbatar da cewa an gabatar da sakamakon taron kasashen Larabawa ga duniya yadda ya kamata.”

Taron dai na da nasaba ne da shawarar da Shugaban Amurka Donald Trump ya bayar na kwace zirin gaza dama tilasta wa Falasdinawa barin Zirin su koma Jordan da Masar.

Trump Ya bayyana shirin ne yayin wani taron manema labarai a fadar White House a farkon watan Fabrairu tare da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da ya ziyarci Amurka.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen Larabawa Abdelatty ya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar KAsuwanci Da HKI
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa