Aminiya:
2025-08-02@04:23:14 GMT

Zargin Almundahana: Kotu ta ba da belin Farfesa Usman

Published: 27th, February 2025 GMT

Wata Babbar Kotu a Abuja, ta bayar da belin tsohon shugaban Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, wanda ake tuhuma da almundahana.

A ranar Alhamis, Mai Shari’a Chinyere Nwecheonwu, ta bayar da umarnin sakin Farfesa Usman daga gidan gyaran hali na Kuje bayan an cika sharuɗan belinsa.

Boko Haram: An lalata gidaje da makarantu a ƙauyukan Adamawa Malaman Jami’ar Sakkwato sun tsunduma yajin aiki

Hukumar EFCC ce, ta gurfanar da shi kan tuhume-tuhume guda biyar da suka haɗa da zargin karkatar da kuɗaɗe.

Ana zargin ya amince wajen sayen motoci a kan Naira miliyan 49.2 maimakon Naira miliyan 30 da aka ware a matsayinsa na shugaban NHIS a 2016.

EFCC, ta kuma ce Farfesa Usman ya bai wa wani kamfani mai suna Lubekh Nigeria Limited kwangilar yaɗa labarai da hulɗa da jama’a ta Naira miliyan 17.5 ta hannun ɗan uwansa, Khalifa Hassan Yusuf.

Duk da haka, Farfesa Yusuf ya musanta dukkanin zarge-zargen da ake yi masa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Usman

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa

Shugaba Bola Tinubu ya amince da naɗin Olumode Samuel Adeyemi a matsayin sabon Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa.

Sabon shugaban hukumar zai fara aiki a hukumance daga ranar 14 ga watan Agusta, 2025.

Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri  Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno

An sanar da wannan naɗin ne a ranar Laraba cikin wata sanarwa da Hukumar CDCFIB, ta fitar, wacce sakatarenta, Abdulmalik Jibrin, ya rattaba wa hannu.

Wannan naɗin na zuwa ne bayan da shugaban hukumar na yanzu, Injiniya Abdulganiyu Jaji Olola, ke shirin ritaya a ranar 13 ga watan Agusta, 2025, bayan cika shekaru 60 a duniya.

Olumode Samuel Adeyemi yana da ƙwarewa da gogewa a aikin kashe gobara.

Ya fara aikinsa a Hukumar Kashe Gobara ta Abuja, kafin daga bisani ya koma Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa, inda ya bi matakai har ya kai matsayin Mataimakin Shugaban Hukumar a sashen kula da ma’aikata.

A tsawon lokacin da ya shafe yana aiki, ya samu horo da ƙwarewar da ake buƙata a cikin gida da kuma waje.

Haka kuma ya riƙe muƙamai daban-daban a hukumar, kuma memba ne a ƙungiyoyi irin su ANAN, Cibiyar Gudanar da Harkokin Kamfanoni ta Ƙasa, Cibiyar Gudanar da Harkokin Jama’a ta Ƙasa, da kuma Cibiyar Kula da Kuɗaɗe ta Ƙasa.

Hukumar ta yaba wa shugaban da zai ritaya, bisa gudunmawar da ya bayar da kuma irin shirye-shiryen da ya jagoranta a lokacin da yake shugabancin hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
  • Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya
  • Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara Ɗaya
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa