Leadership News Hausa:
2025-06-15@13:17:11 GMT

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (8)

Published: 22nd, February 2025 GMT

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (8)

Ana matukar bukatar jami’an ilimi saboda kuwa sune suke da alhakin tabbatar dukkan tsare tsaren ilimi da manufofi ana amfani da su kamar yadda ya kamata.Suna aiki da Shugabannin makarantu da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da dalibai suna msaun nagartaccen ilimi.

Hakanan ma jami’an ilimi ma na bukatar su rika gabatar da horarwa ga Malamai da sauran ma’aikata kkan irin nau’oin dabarun na koyarwa da ba a dade da fara aiki da su ba.

Ganin yadda ake ta kara maida hankali kan ilimi mai nagarta da kuma irin sauye sauyen da ke yawan samu ta bangaren ilimi,hakan shi yasa ake ta kara yawan bukatar jami’an ilimi shi yasa za a ci gaba da samun hakan a shekaru masu zuwa.

Abubuwan da ake bukata daga jami’in ilimi

Shi da jami’in ilimi abubuwan da ke bukatar ya mallaka saboda irin gudunmawar da yake badawa a ko wace rana wajen daukar mataki.Babban abinda ake bukata kowace rana ana tabbatar da kowa da kowa yana samun irin ilimi mai nagarta da ya dace ya samu,ba ta re da la’akari da cewar shi wanene ba,ya ya yake,mai arziki ne ko kuma shi wani tantirin matalauci ne, ko kuma wane irin tafarkin addini yake bi.

Jami’an ilimi dole ne su tabbatar da bi dukkan shharuddan ilimi kamar yadda ya kamata, ba tare da wada wata maganar da bata kamata a yada ta ba, wajen huldarsu, dalibai, iyalai, da kuma abokan aiki.Bayan haka ma duk abinda da za su yi wanda ya shafi daukar mataki abu mafi dacewa shi ne su yi hakan ta byadda abin zai taimakawa mai koyo, sai kuma tafiyar da lamarin ilimi da gaskiya, ba tare da nuna wani bambanci ba, duba yadda lamrin ilimi yake, da kuma hanyar bada rahoto.

Jami’an ilimi bu da ake fison gani suna yi shi ne su guji nuna duk wani abinda ya sabawa gaskiya babu kuma wani bambanci ba, a duk wata hanya ta gudanar da aikinsu.

Hanyar da mutum zai bi domin ya zama jami’in ilimi

Idan har mutum yana bukatar zama jami’in ilimi ya kamata ya samu mallakar satifiket din digiri kan lamarin daya shafi ilimi ko kuma wani abu mai nasaba da shi, wannan ya hada da ya kasance yana da kwarewa kan lamarin daya shafi koyarwa ma’ana ko ya taba aikin koyarwa a cikin aji.

Wasu jami’an ilimin ana da bukatar su samu mallaki takardar shedar ko lasin da yake nuna cewar da akwai wani sashe ko bangare na ilimi da suka kware ko maida hankalinsu akai.

Hakanan ma idan mutum ya sani kan kwarai yadda zai iya tafiyar da mu’amalar sa da mutane, da kuma yadda yake ba lamarin muhimmanci sosai, da kuma irin wayo na yadda zai iya yin aiki da sauran abokan aikinsa subna daga cikin abubuwan da ake bukata ya mallaka domin ya samu nasara kan aikinsa. Idan dai an mallaki karatun da samun ilimin da ake bukata da kuma kwarewa, sai kuma dabaru,wadanda suke bukatar a dauke su domin su zama jami’an ilim suna iya fara neman aikin ta fannin da ba za su taba yin dana- sani ba.

Wannan shi ne rubutu na karshe kan ayyukan jami’an ilimi da muhimmancinsu, inda kuma muka fara da halayen kirki 14 da ake bukatar Malamin makarnta ya kasance da su.

Haleyen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Wurin Malamin makaranta (1)

Idan ka fara yin tunani kan ilimin ka wanda ka samu na can baya ba za ka taba mantawa da wani Mlamai ba wanda ya zame maka wanda za ka rika tunawa da shi domin yana baka ko ya baka kwarin gwiwa,kana kuma koyi da yadda yake tafiyar da rayuwar aikinsa ta Malamin makaranta.

Me yiyuwa shi ko Farfesa ne wanda ya sa ka canza sauya irin aikin da ka ke son yi, ko kuma Malaminne wanda yake koyawa yara kananan wanda saboda irin halin kirkin shi ne ya sa ma ka samu sauyi a rayuwar ta yaro karami.Kai wannan ma duk ba wani abu bane duk dai wani kokarain da ka yi a wani darasin da ake koya maka, akwai wasu halaye abubuwan da ake bukatar Malamin makaranta ya Kasane yana da sun a dabarun da za su taimaka ma sa wadanda za ayi magana kan su a cikin wannan maudu’in, wadannan kamar yadda aka tsara bayyana su ,sune wasu alamun halayen kirki da ake bukatar ace Malamin makaranta ya mallake su ko ace yana da su.

Sai a ci gaba da karantawa yayin da kuma za a hadu da wasu halayen kirki 14 da ake son Malamin makaranta ace yana da su kamar yadda masana ilimi suke bukatar haka shekara 2032 har ma gaba da hakan.

Kai abin ma ha rya zarce haka domin kuwa har ma da irin nau’in takardun ilimin da ake bukata kafin wani ya cancanci zama Malamin makaranta.Ko dai kana bukatar ka kara samun dabaru ne na salon koyarwa ,yadda za a koyar ya kuma zama da’iman ne ka mallake su, ko kuma halaye ne ya kamata ace kana da irinsu, koma dai me nene ya dace ka yi, wadannan shawarwarin ko nau’oin halayen su ne ake bukatar su zama maka kamar wata manuniya ta yadda za ka rika bunkasa ilimin ka, saboda ta hakan ne za ka samu damar inganta takardar da ke bada bayanai na ko wanene kai ta bangaren ilimin da ka mallaka ko kake da shi.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ayyuka Malamin makaranta kamar yadda ake bukatar

এছাড়াও পড়ুন:

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

Sai dai, ya sanar da cewa, ya janye kurin ne, bayan ya tuntubi daidaikun mutane da sauran kungiyoyi a daukacin fadin kasar.

Halin girma da dakkun da Shugaba Abba ya nuna na janye wannan kurin bayan korafe-korafen alummar asar kasar, babu shakka janyewar abu ne, da ya dace, musamman duba da cewa, tursawa ‘yan kasa a tsarin Dimokiradiyya abu ne da bai dace ba, domin kuwa a tsarin dimokiradyya ana bai wa ‘yan zabin abinda zuke bukata, wanda hakan ya sabawa batun tilasta masu yin zabe.

Bugu da kari, batun fitar jama’a yin zabe, abu ne da ake bukatar a rinka wayar da kan ‘yan kasa da nuna masu amincewa, amma bai wai ace za a tilasata su, yin zaben ba da kuma cewar, za a hukunta su ba.

Sashe na 77 (2) a cikin baka da kuma sashe na 132 (5) a cikin baka, na kundin tsarin mulkin kasar nan na1999 da aka sabunta, sun bai wa ‘yan Nijeriya da suka kai shekaru 18 kuma suke zaune a kasar kada ‘yancin yin zabe.

Sai dai, rukunin ‘yan kasar da kundin bai bai wa wannan ‘yancin ba sune, wadanda ba su yi rijista sunayen su a hukumar INEC ba da wadanda aka yankewa hukuncin kisa sai kuma masu tabin hankail.

Wani abin takaici a kasar shi ne, yadda a ranar zabuka a kasar wadda kuma aka haramta zirga-zirgar mutane da gudanar da hada-hadar kasuwanci, amma wasu ‘yan kasar sukan yi burus da wannan haramcin, su fita a ranar zabukan don gudnar da hidindumin su, inda kawai ake ganin wasu, ‘yan kalilan ‘yan kasar ne, ke fita yin zaben.

Abin har ya zama jiki a Nijeriya, domin kusan sama da shekaru uku da suka gabata, duk lokacin da za a gudanar da zabukan gama gari, ana fuskantar karancin masu fitowa kada kuri’a, wanda haka ke nuna cewa, ana samun babban kalubale.

Misali, a 2015, duba da yawan adadin ‘yan kasar da suka canci kada kuri’a su miliyan 67.42, miliyan 29.43 ne kacal, suka fito jefa kuri’a wanda wannan adadin ya nuna cewa, kaso 65 ne kacal, suka kada kuri’unsu.

Bugu da kari, a 2019, wadanda suka canci kada kuri’a su miliyan 84 ne kacal, ba su fito kada kuri’a ba, inda miliyan 28.61 ne kacal, suka fito jefa kuri’arsu, wanda hakan ya nuna sun kai kaso 34.75.

Duba da yadda ‘yan kasar suka nuna matukar bukatar son fita zaben 2023, amma wadanda suka fita zaben, amma miliyan 24.97 ne kawai suka fita zaben wanda hakan ya nuna cewa, kaso 26.72 ne kawai, suka fita zaben, daga cikin wadanda suka canci yin zaben su miliyan of 93.47.

A batu na gaskiya, adadin masu fita zabe a Nijeriya ya yi kasa matuka, idan aka kwatanta da yadda wadanda suka canci kada kuri’a a kasashen Afirka ke yin Farar dango don fita zaben.

Alal misali, alkaluman zabukan da aka gudanar a kasashe kamar irinsu Rwanda, ta kasance tana da kaso 98.2, Gabon na da kaso 59, Liberiya na da kaso 70.

Kazalika, Sierra Leone na da kaso 75 Jamhuriyar Kongo na da kaso 42, Zimbabwe na da kaso 68.86, Afirka ta Kudu na da kaso 65, Masar na da kaso 66.88, sai kuma and Ghana wadda take da kaso 60.

Irin wadannan alkaluman a Nijeriya, batun yasha ban ban, domin a zaben 2023, an samu kaso 26.74 ne.

Zaben shugaban na 2023, tamkar anyi shi ne, na kusan gumurzu wanda shuaban kasar mai ci Bola Tinubu, ya lashe zaben, ta hanyar samun kuri’u 8,794,726 kacal, duk da cewa, Nijeriya na da wadanda suka kai munzalin kada kuri’a, su sama da miliyan 100.

Mai yawa, saboda irin wannan abin damuwar na rashin fita zaben ne, hakan ya sanya Abbas Tajudden da takwaransa Daniel Asama Ago, suka gabatar da dakataccen kudurin na tilasta ‘yan kasar da suka kai munzalin jefa kuri’a fita, domin sauke ‘yancinsu, da kundin tsarin mulkin kasar ya ba su.

Kin fita yin zaben da wasu ‘yan kasar da suke kai munzalin kada kuri’a, abu ne da bai dace ba.

A bisa matakin farko, abinda yafi dacewa a gano shi ne, shin me ke hada ‘yan kasar suka canci kada kuri’a ba su fita yin zaben, sannan kuma a lalubo da mafitar magance hakan.

Sai dai, wani hanzari ba gudu ba, za a iya cewa, ba su fita zuwa sauke nauyin na su ne, gazawar yadda ake tsara komai na gudanar da zabukan.

Karin wani abin takaicin shi ne, yadda wasu ‘yan zamalar ‘yan takara ‘yan siyasa ke hada baki da jami’an zabe, jami’an tsaro, inda kuma daga baya-bayan nan, suke hada baki da wasu Alakalai domin a tabka choge, a murda zabukan.

Irin wannan karfa-karfar da kuma murde zabuka ne, ke janyo karya masu Guiwar masu jefa kuri’ar, domin a bai wandanda ba su ci zaben nasara ba, wanda a lokuta da dama, wasu zabukan, ba a kammala kidaya kuri’un da aka kada.

Bugu da kari, a gefe daya kuma akwai matsalar ‘yan bangar siyasa da ke tayar da yamusti a Rumfunan zabe musamman domin su kare rayukansu daga aukwar ‘yan bangar siyasa da matsalar sayen kuri’u da kuma wallafa labarukan karya na sakamakon zabukan.

Hakazalika, wani batun mai ban haushi shi ne, na rashin hukuntan wadanda suka karyar dokokin zaben.

Karin wani abin takaicin shi ne, na yadda jam’iyyun kasar ba su da dabi’ar ilimantar da masu jefa kuri’a kuma ba su wani takamai-man shirye-shirye da suka tanada, domin yin hakan, sai dai kawai, su buge da yin farfagandar siyasa, wanda idan sun dare madafun iko, su yi watsi da magoya bayansu.

Akwai kuma batun kalubalen rashin samun samun yin rijitsa domin samun katin yin zabe wato PBC.

A bisa ra’ayin wannan Jaridar, mai makon batun matsawa wadanda suka munzalin jefa kuri’a don su yi zaben ba, kamata ya yi ‘yan Majalisar su gabatar da kudurin da zai sanya a sanya wa ‘yan kasar da suka cancanci kada kuri’a sha’awar fita sauke nauyin na su.

Yin haka ne, kadai, zai tabbatar da matsayin Hukumar Zabe ta kasa INEC, tabbacin cewa, Hukuma ce, mai cin gashin kanta.

Kazalika, ya zama wajbi INEC ta kara inganta tsare-tsaren ta kuma dole ne, duk wani jami’ain tsaro da ‘yan siyasar da aka samu da taka dokokin zabe, an hukunta su.

Wannan Jaridar na da yakinin cewa, ‘yan Nijeriya na son fita yin zabe, amma yadda ba a gudanar da zabukan a bisa gaskiya ne ke kara janyo wadanda suka canci kada kuri’ar, ba su fita, domin sauke nauyinsu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba