Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Suke Da Hakkin Yanke Shawarar Makomar Kaarsu Ba Amurka Ba
Published: 21st, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Iran ce zata yanke shawara a nan gaba kan matsayin kasarta, ba Trump ba
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a yammacin jiya Alhamis ya jaddada cewa: Iran ce take da hakkin yanke shawara kan makomarta ba Trump ba, yana mai jaddada wajabcin sauya ra’ayi domin dakile duk wani takunkumin da Trump ya kakabawa kasarsa.
A jawabin da shugaba Pezeshkian ya gabatar a wajen taron shugabannin lardin Tehran ta yamma da majalisar gudanarwa ta garuruwan Mallard, Shahriar da Quds, shugaba Pezeshkian ya bayyana cewa, ma’anar gudanarwa ita ce sanin damammaki da barazana a ciki da wajen kasar da kuma sanin irin karfi da ake da shi.
Shugaban kasar ya jaddada cewa: Trump na fadin wani abu, kuma wasu mutane sun saba da abin da Trump yake so. Mene ne Trump yake son aikatawa? A nan mu ne za mu yanke shawarar yadda za mu tafiyar da makomarmu. Idan ba Iran ba ta canza ra’ayinta ba, to, ta sanya wa kanta takunkumi a hukumance, amma idan ta sauya ra’ayinta, Trump ba zai kai ma burinsa ba, kuma komai yawan takunkumin da zai Sanya kan kasar Iran.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce sojojin kasar Iran ba za su sararawa gwamnatin Isra’ila ba.
Jagoran ya bayyana hakan ne a wani sakon bidiyo ga al’ummar Iran ranar Juma’a biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta yi kan kasar wanda ya kashe fararen hula, masana kimiyya da kwamandojin soji.
Ayatullah Khamenei ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila ba za ta kubuta daga wannan aika-aika ba, yana mai tabbatar wa al’ummar Iran cewa ba za a yi sakaci kan hakan ba.
Jagoran ya jaddada cewa muguwar gwamnatin sahyoniya ta tafka babban kuskure, sannan kuma shelanta yaki ne kan Iran.
Ayatullah Khamenei ya ci gaba da cewa: dukkanin jami’an kasar Iran da bangarori daban-daban na siyasa da kuma al’ummar Iran suna da ra’ayi daya dangane da wajabcin daukar wani mataki mai karfi wajen tunkarar gwamnatin sahyoniya ta ‘yan ta’adda.
Jagoran ya kara da cewa, bai kamata gwamnatin Isra’ila ta yi tunanin cewa ta ci bulus ba, kuma komi ya wuce.