Tattaunawa Kan Ƙurajen Fuska (Pimples)
Published: 17th, February 2025 GMT
Kiyaye taruwar maiƙo da kwayoyin cuta a fuska da kirji. Wannan kan dan yi wahala amma ta wadannan dabaru za a samu nasara:
1- Rage maiƙo a cikin abinci. Misali, idan aka soya wani abinci, yana da kyau a tsane mai da mayanin kicin wafif ko tawul ko tushu mai tsabta kafin a ci. Idan an yi haka an rage man kusan da kashi hamsin cikin dari ko ma fiye.
2- Yin amfani da sabulu mai kashe kwayoyin cuta wajen wanke fuskar safe da yamma.
3- Shan kayan itatuwa da cin ganyayyaki a kai –a-kai ya kan tsane maikon cikin jini ya kara karfin garkuwar jiki wajen yakar kwayoyin cuta.
4- Ga wanda wadannan
Dabaru ba su yi musu aiki ba, za su iya zuwa su nemi man shafawa na fuska da kirji mai dauke da sinadarin benzoyl perodide na shafawa safe da yamma bayan an wanke fuska.
5- Idan hakan ta ki wadatarwa sai an je asibiti an hada da karbar magungunan kashe kwayoyin cuta. 6- Ga wadanda wannan ma bai yi aiki ba, akwai dai magunguna masu karfi, har ila yau irin samfurin bitaman ‘A’ da ake kira isotretoin da ake rubutawa a asibiti. Akan samu nasara sosai idan aka jarraba wadannan. Amma ba a ba wa mai juna biyu shi.
7- Ba a so a rika matse kurajen saboda hakan kan iya jawo tabo, an fi so a bar su su fashe da kansu sai a wanke wurin. Allah ya sa mu dace
কীওয়ার্ড: Kuraje Tattaunawa kwayoyin cuta
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON Ta Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da NUJ Don Inganta Kwarewar Aiki
Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi ta Jihar Jigawa (ALGON) ta yi alkawarin kafa kyakkyawar haɗin gwiwa da ƙungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar, domin inganta ƙwarewar jami’an hulɗa da jama’a a fadin jihar.
Shugaban ALGON, Farfesa Abdurrahman Salim ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi shugabannin NUJ a wata ziyarar girmamawa da suka kai masa a sakatariyar ALGON da ke Dutse, babban birnin jihar.
Farfesa Salim ya jaddada muhimmancin yada bayanai a harkokin mulki da kuma isar da ayyuka ga jama’a, yana mai cewa samun ingantacciyar sadarwa na da matuƙar muhimmanci.
A cewarsa, bai wa jami’an hulɗa da jama’a horo da ƙwarewa zai taimaka wajen sauƙaƙe isar da sahihan bayanai ga al’umma.
Farfesa Salim ya tabbatar wa NUJ da cikakken goyon baya da haɗin gwiwar ALGON wajen ƙarfafa ƙwarewar jami’an bayanai, domin su daidaita da sauye-sauyen da ke faruwa a duniyar kafafen yaɗa labarai.
Tun da farko, Shugaban NUJ na jihar Jigawa, Kwamared Isma’il Ibrahim Dutse, ya ce shugabannin ƙungiyar sun kai ziyarar ne domin neman haɗin kai da goyon baya daga ALGON.
Ya ce NUJ ta yi amanna cewa sadar da bayanai na da matukar muhimmanci wajen tafiyar da mulki da kuma isar da ayyuka ga jama’a.
Usman Mohammed Zaria