HausaTv:
2025-05-27@18:37:51 GMT

Hamas Ta Saki ‘Yan Isra’ila Uku Kan Falasdinawa 369 A Musayar Fursunoni Ta Shida

Published: 15th, February 2025 GMT

kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta mika wasu ‘yan Isra’ila uku da ta yi garkuwa da su ga kungiyar agaji ta Red Cross a wani musayar fursunonin da aka sako Falasdinawa 369 a wata musanya ta baya-bayan nan a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

An saki ‘yan Isra’ilan uku a birnin Khan Yunus da ke kudancin Gaza, inda Isra’ilawan suka yi jawabi ga jama’a kafin mika su ga kungiyar agaji ta Red Cross.

Sakin dai shi ne na shida tun bayan da tsagaitawar ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu bayan fargabar da ake yi a makon da ya gabata cewa yarjejeniyar ta kusa rugujewa bayan da Isra’ila ta ki ba da isassun kayan agaji a Gaza.

Yawancinsu fursunoni falasdinawan da aka saki wadanda aka kama ne a zirin Gaza bayan harin ba zata da kungiyar ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba.

Yarjejenitar tsagaita bude wuta ta shiga cikin tsaka mai wuya tun bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya tayar da cece-kuce kan “kwace” Gaza, da tilastawa mutanen Zirin kaura zuwa Jordan da kuma Masar.

A karkashin Yarjejeniyar tsagaita bude wutar ana sa ran sakin ‘yan Isra’ila 33 yayin kan fursuninin falasdinawa 1,900.

Kawo yanzu an saki Isra’ilawa 16, kan fursunoni 765 na Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Shirin  HKI Da Amurkan  Na Raba Kayan Agaji A Gaza Ya Yi Murabus

Jaridar ” Up Isra’el” ta buga labarin cewa; shugaban cibiyar Ayyukan Agaji A Gaza” wacce ke karkashin Amurka da Isra’ila”  ya yi murabus saboda abinda ya kira rashin gaskiya da ‘yanci a cikin Shirin.

Jaridar ta ambato  Jake Wood yana cewa; Ba abu ne mai yiyuwa ba a aiwatar da Shirin agaji a Gaza, sannan kuma a ce za a yi aiki da ka’idojin ‘yan’adamtaka, tsaftar aiki, da cin gashin kai, da abubuwa ne wadanda ba zan taba ja da baya a kansu ba.”

Wood ya yi kira da a yi ayyukan gabatar da kayan agajin a cikin yankuna masu yawa na Gaza,a kuma a  yi aiki da dukkanin hanyoyin gabatar da taimako.”

Wood ya bayyana cewa; Tun watanni biyu da su ka gabata ne aka tuntube shi domin ya jagoranci wannan cibiyar,saboda kwarewar da yake da ita a fagen ayyukan agaji, sannan ya kara da cewa: ” Daidai da sauran mutane masu yawa a duniya, na firgita, na kuma yi bakin ciki saboda yadda na ga  ake fama da yunwa a Gaza,sannan kuma a matsayina na jagora a fagen ayyukan agaji na ji cewa  nauyi ne da ya rataya a wuyana in yi abinda zan iya saboda rage wahalhalun da mutane suke cki.”

Jaridar ta “Up-Isra’el” ta kuma ce; Ajiye aiki da Wood ya yi, babban ci baya ne ga Isra’ila, kuma ya zuwa yanzu babu tabbacin ko wannan cibiyar za ta yi aikinta.”

Da akwai alamar tambaya akan ayyukan cibiyar wacce ba a adade da kafa ta ba, sannan kuma babu cikakkiyar masaniya akan inda ta samo kudin da su ka kai dala miliyan 100.

MDD dai ta ce ba za ta shiga cikin ayyukan agaji a Gaza ba, matukar ba za a bi dokokin kasa da ka sa ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  •  Sojojin HKI Sun Yi Wani Sabon Kisan Kiyashi A Gaza
  • Shugaban Shirin  HKI Da Amurkan  Na Raba Kayan Agaji A Gaza Ya Yi Murabus
  • ‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa
  • Ukraine Da Rasha Sun Yi Musayar Fursinoni Tsakaninsu Irinsa A Karon Farko
  • Warware Basussuka: WAEC DA NECO Sun Saki Sakamakon Ɗaliban Zamfara Na Shekara Biyar
  • Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta
  • Hamas ta yi tir da kiran da dan majalisar dokokin Amurka ya yi na kai farmakin nukiliya a Gaza
  • Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane 299