HausaTv:
2025-07-13@03:38:49 GMT

Hamas Ta Saki ‘Yan Isra’ila Uku Kan Falasdinawa 369 A Musayar Fursunoni Ta Shida

Published: 15th, February 2025 GMT

kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta mika wasu ‘yan Isra’ila uku da ta yi garkuwa da su ga kungiyar agaji ta Red Cross a wani musayar fursunonin da aka sako Falasdinawa 369 a wata musanya ta baya-bayan nan a karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

An saki ‘yan Isra’ilan uku a birnin Khan Yunus da ke kudancin Gaza, inda Isra’ilawan suka yi jawabi ga jama’a kafin mika su ga kungiyar agaji ta Red Cross.

Sakin dai shi ne na shida tun bayan da tsagaitawar ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu bayan fargabar da ake yi a makon da ya gabata cewa yarjejeniyar ta kusa rugujewa bayan da Isra’ila ta ki ba da isassun kayan agaji a Gaza.

Yawancinsu fursunoni falasdinawan da aka saki wadanda aka kama ne a zirin Gaza bayan harin ba zata da kungiyar ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba.

Yarjejenitar tsagaita bude wuta ta shiga cikin tsaka mai wuya tun bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya tayar da cece-kuce kan “kwace” Gaza, da tilastawa mutanen Zirin kaura zuwa Jordan da kuma Masar.

A karkashin Yarjejeniyar tsagaita bude wutar ana sa ran sakin ‘yan Isra’ila 33 yayin kan fursuninin falasdinawa 1,900.

Kawo yanzu an saki Isra’ilawa 16, kan fursunoni 765 na Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

A yau Alhamis, aka bude taron ministoci na dandalin tattaunawa game da wayewar kai a duniya a birnin Beijing, inda aka mayar da hankali kan muhimmancin mabanbantan al’adu da fahimtar juna wajen samun ci gaban harkokin dan Adam.

Taron na yini biyu mai taken “Kiyaye bambancin wayewar kan al’adun bil’adama don samun zaman lafiya da ci gaban duniya” ya ja hankalin baki sama da 600 daga kasashe da yankuna 140.

Yayin wasu kananan taruka da za su gudana lokaci guda a karkashin dandalin, mahalarta za su lalubo muhimmiyar rawar da musayar al’adu daban-daban da fahimtar juna ka iya takawa ga ingiza dunkulalliyar duniya da inganta ci gaban duniyar da kwanciyar hankali da gadon al’adu da kirkire-kirkire da fahimta da abota tsakanin jama’a da samar da ci gaban kimiyya da fasaha da musaya tsakanin masana. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra\ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa A Zirin Gaza
  • DSS ta saki Ɗan Bello bayan ta kama shi a Kano
  • NYT: Natanyahu Yana Tsawaita Yaki A Gaza Don Ci Gaba Da Kasancewa Kan Iko A HKI
  • ‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja
  •   Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i Kadan
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Somaliya: Kungiyar Al-Shabab Ta Kai Wa Barikin Soja Hari A Birnin Magadishu
  • An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza