Katsina ta zama cibiyar haɗin kan ƙabilun ƙasa a Arewa — Gwamna Radda
Published: 9th, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya tabbatar da naɗin Sarkin Yarbawan Funtuwa, Oba Alhaji Murtala Sani Adeleke a matsayin sabon Sarkin Yarbawan Jihohin Arewa 19 har da Abuja.
Mataimakin Gwamnan JIhar Katsina, Malam Faruk Lawal Jobe ne ya tabbatar da naɗin a madadin gwamnan a lokacin da yake karɓar baƙuncin tawagar Sarakunan Yarbawan Arewa da suka miƙa masa takardar amincewarsu ga zaɓen Alhaji Murtala Sani Adeleke a matsayin sabon Sarkin Yarbawan Arewa a fadar gwamnati da ke Katsina.
Gwamnan ya nuna matuƙar farin ciki da jinjina wa yadda aka gudanar da zaɓen shugabannin Majalisar Sarakunan Yarbawan na Arewa lami lafiya.
Ya ce, zaɓen wanda shi ne irin sa na farko a tarihin zaman ƙabilun Yarbawa a Arewacin ƙasar, ya nuna alamar ɗorewar haɗin kan al’ummomin ƙasa ne da ci gabansu.
Ya ce, “Wannan muhimmiyar nasara ce ga Jihar Katsina da al’ummar ƙabilun Yarbawa da ke zaune a Jihohin Arewacin ƙasa baki ɗaya.”
Da yake yi wa Aminiya ƙarin haske, Sarkin Yarbawan Jihar Kano, Oba Murtala Alimi Otisese, wanda aka zaɓa a matsayin mataimakin Sarkin Yarbawan Arewa kuma shugaba na shirye-shiryen bikin wankan sarauta, ya ce, “a ranar Lahadi mai zuwa 15 ga watan Fabrairu ne za mu gudanar da wannan biki a birnin Abuja, inda za a miƙa wa sabon Sarkin Yarbawan Arewa Oba Murtala Sani Adeleke da ’yan majalisarsa takardun shaida (Satifiket) domin tabbatar da naɗinsu a hukumance.”
Oba Murtala Alimi Otisese ya ce, “muna sa ran halartar wasu sarakunan Yarbawa da manyan mutane daga Jihohi 6 na Kudu maso Yamma da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na ƙasa zuwa wajen bikin a Abuja.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa Dikko Umar Radda Jihar Katsina Yarbawa Sarkin Yarbawan
এছাড়াও পড়ুন:
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
Da yake tuna tarihin siyasarsa a matsayin daya daga cikin gwamnonin adawa a farkon shekarun 2000, Tinubu ya sake jaddada matsayinsa a matsayin mai kare dimokradiyyar jam’iyyun adawa.
Ya kuma mika godiyarsa ga magabacinsa, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, bisa yadda ya fahimci tare da gyara abin da ya bayyana a matsayin “kuskuren zaben 1993,” wanda aka yi imani da cewa, Cif Moshood Abiola da Alhaji Babagana Kingibe ne suka lashe amma gwamnatin soja ta soke zaben.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp