Aminiya:
2025-04-30@23:43:46 GMT

Katsina ta zama cibiyar haɗin kan ƙabilun ƙasa a Arewa — Gwamna Radda

Published: 9th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya tabbatar da naɗin Sarkin Yarbawan Funtuwa, Oba Alhaji Murtala Sani Adeleke a matsayin sabon Sarkin Yarbawan Jihohin Arewa 19 har da Abuja.

Mataimakin Gwamnan JIhar Katsina, Malam Faruk Lawal Jobe ne ya tabbatar da naɗin a madadin gwamnan a lokacin da yake karɓar baƙuncin tawagar Sarakunan Yarbawan Arewa da suka miƙa masa takardar amincewarsu ga zaɓen Alhaji Murtala Sani Adeleke a matsayin sabon Sarkin Yarbawan Arewa a fadar gwamnati da ke Katsina.

Ta kashe saurayinta saboda ya gaisa da tsohuwar abokiyar karatunsa Abba ya naɗa sabon Sakataren Gwamnatin Kano

Gwamnan ya nuna matuƙar farin ciki da jinjina wa yadda aka gudanar da zaɓen shugabannin Majalisar Sarakunan Yarbawan na Arewa lami lafiya.

Ya ce, zaɓen wanda shi ne irin sa na farko a tarihin zaman ƙabilun Yarbawa a Arewacin ƙasar, ya nuna alamar ɗorewar haɗin kan al’ummomin ƙasa ne da ci gabansu.

Ya ce, “Wannan muhimmiyar nasara ce ga Jihar Katsina da al’ummar ƙabilun Yarbawa da ke zaune a Jihohin Arewacin ƙasa baki ɗaya.”

Da yake yi wa Aminiya ƙarin haske, Sarkin Yarbawan Jihar Kano, Oba Murtala Alimi Otisese, wanda aka zaɓa a matsayin mataimakin Sarkin Yarbawan Arewa kuma shugaba na shirye-shiryen bikin wankan sarauta, ya ce, “a ranar Lahadi mai zuwa 15 ga watan Fabrairu ne za mu gudanar da wannan biki a birnin Abuja, inda za a miƙa wa sabon Sarkin Yarbawan Arewa Oba Murtala Sani Adeleke da ’yan majalisarsa takardun shaida (Satifiket) domin tabbatar da naɗinsu a hukumance.”

Oba Murtala Alimi Otisese ya ce, “muna sa ran halartar wasu sarakunan Yarbawa da manyan mutane daga Jihohi 6 na Kudu maso Yamma da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na ƙasa zuwa wajen bikin a Abuja.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Dikko Umar Radda Jihar Katsina Yarbawa Sarkin Yarbawan

এছাড়াও পড়ুন:

Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya

Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya ta naɗa Sheikh Bashir Aliyu Umar a matsayin shugabanta bayan rasuwar Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.

Wata sanarwa da majalisar ta fitar a yau Laraba ta ce an amince da shuagabancin Dokta Bashir ne kai-tsaye saboda kasancewarsa mataimakin shugaba.

A ranar Litinin ne Sheikh Hadiyyatullah ya rasu yana da shekara 81 a Jihar Osun.

“Nan gaba za a sanar da mataimakin shugaban,” in ji sanarwar da Nafiu Baba Ahmed ya sanya wa hannu a matsayin sakataren majalisar.

Sheikh Bashir sanannen malami ne kuma shi ne babban limamin masallacin Juma’a na Al-Furqan da ke Alu Avenue a Unguwar Nasarawa ta Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara