Mata a Karamar Hukumar Danja suna kira ga Gwamnatin Jihar Katsina da ta gyara hanyar Tsangamawa a Babban Rafi saboda yawan rasuwar mata masu juna biyu da jariransu.

 

Sun yi wannan kira ne a yayin wani taron gaggawa da manyan jiga-jigan al’umma suka shirya domin tattauna matsalar da ta dade tana addabar jama’a – hanyar Tsangamawa.

 

Hanyar Tsangamawa da ke Babban Rafi, Karamar Hukumar Danja, Jihar Katsina, ta haddasa mutuwar mata masu juna biyu da jariransu, musamman a lokacin damina.

 

Duk da yawan koke da rokon gwamnati, har yanzu ba a dauki matakin gyara hanyar ba.

 

A wata hira da suka yi da Radio Nigeria, wasu daga cikin matan yankin sun bayyana cewa mata masu juna biyu da jariransu ne suka fi fuskantar barazana, musamman a lokacin damina, saboda wahalar kai su asibiti sakamakon mummunan halin da hanyar take ciki.

 

Duk da cewa akwai cibiyar kiwon lafiya a yankin, ginin ya lalace, kuma yawancin ma’aikatan jinya da na lafiya ba sa iya zuwa aiki akai-akai saboda matsalar hanya.

 

Wata uwa mai ‘ya’ya hudu a yankin, Hajara Ibrahim, ta bayyana bakin cikinta, tana mai cewa har yanzu babu wata gwamnati da ta nuna musu tausayawa, duk da cewa suna da hakkin rayuwa mai inganci.

 

Malama Tayyiba Muktari daga Babban Rafi ta bada labarin yadda ta tsira da kyar a cikin juna biyunta na baya, inda ta ce nufin Allah ne ya sa ta tsira, sannan ta roki Gwamnatin Jihar Katsina da ta dauki matakin gaggawa kan hanyar.

 

Haka kuma, wata mata daga yankin, Fatima Abdullahi, ta koka kan yadda mummunan yanayin hanyar ke hana mazajensu fita neman abin dogaro da rayuwa.

 

Haka nan, wani tsohon jami’in lafiya a Jihar Katsina, Dr. Haruna Abubakar, ya bukaci Gwamnatin Jihar Katsina da ta saka aikin gina hanyar Tsangamawa, Babban Rafi a kasafin kudin bana saboda mahimmancinsa ga al’umma.

 

Matan yankin sun roki Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Dikko Umar Radda, da ya tausaya musu da iyalansu ta hanyar gyara hanyar.

 

Duk da cewa hanyar tana da kimanin kilomita 23 kacal, gwamnatocin baya sun kasa gyarata. Dole ne gwamnati ta fara fifita yankunan karkara wajen bayar da kwangiloli domin inganta rayuwar al’umma.

 

Cov/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jariransu

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa

Gwamnatin Kano ta raba kayayyakin aiki na zamani na kimanin Naira Miliyan 250  ga cibiyoyin horas da sana’o’in hannu biyu da ke Kofar Mata da Gwale, domin yaƙi da shan miyagun kwayoyi da aikata laifuffuka a tsakanin matasa, ta hanyar samar da aikin yi.

Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dakta Yusuf Kofarmata, ya ce an amince da tallafin ne bisa umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf don bunƙasa tsare-tsaren ƙarfafa matasa a jihar.

Ya bayyana cewa an samar da injinan sarrafa fata guda 26 domin cibiyoyin wadanda al’ummar yankunan suka kafa, amma ba su da isassun kayayyakin aiki.

Ya ce Gwamna Yusuf ne ya gina Cibiyar Horaswar ta Gwale  kasancewar nan ce mazabarsa, yayin da Dakta Yakubu Adam ya taka rawa wajen gina ta Kofar-Mata.

Ya ce cibiyoyin za su samar da daruruwan ayyukan yi tare da rage matsalolin zaman kashe-wando da ta’addanci a tsakanin matasa.

 

A nasa jawabin, Ali Musa Kofar-Mata na ƙungiyar IKMA ya gode wa gwamnati bisa wannan gudummawar da ya kira mai sauya rayuwa.

Ya ce cibiyar ta fara ɗaukar matasa maza da mata, kuma horon zai ɗauki watanni uku kafin a shiga sabon zagaye.

 

Abdullahi Jalaluddeen 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata