Lalacewar Hanya Na Janyo Yawan Mutuwar Mata Masu Juna Biyu Da Jariransu A Katsina
Published: 8th, February 2025 GMT
Mata a Karamar Hukumar Danja suna kira ga Gwamnatin Jihar Katsina da ta gyara hanyar Tsangamawa a Babban Rafi saboda yawan rasuwar mata masu juna biyu da jariransu.
Sun yi wannan kira ne a yayin wani taron gaggawa da manyan jiga-jigan al’umma suka shirya domin tattauna matsalar da ta dade tana addabar jama’a – hanyar Tsangamawa.
Hanyar Tsangamawa da ke Babban Rafi, Karamar Hukumar Danja, Jihar Katsina, ta haddasa mutuwar mata masu juna biyu da jariransu, musamman a lokacin damina.
Duk da yawan koke da rokon gwamnati, har yanzu ba a dauki matakin gyara hanyar ba.
A wata hira da suka yi da Radio Nigeria, wasu daga cikin matan yankin sun bayyana cewa mata masu juna biyu da jariransu ne suka fi fuskantar barazana, musamman a lokacin damina, saboda wahalar kai su asibiti sakamakon mummunan halin da hanyar take ciki.
Duk da cewa akwai cibiyar kiwon lafiya a yankin, ginin ya lalace, kuma yawancin ma’aikatan jinya da na lafiya ba sa iya zuwa aiki akai-akai saboda matsalar hanya.
Wata uwa mai ‘ya’ya hudu a yankin, Hajara Ibrahim, ta bayyana bakin cikinta, tana mai cewa har yanzu babu wata gwamnati da ta nuna musu tausayawa, duk da cewa suna da hakkin rayuwa mai inganci.
Malama Tayyiba Muktari daga Babban Rafi ta bada labarin yadda ta tsira da kyar a cikin juna biyunta na baya, inda ta ce nufin Allah ne ya sa ta tsira, sannan ta roki Gwamnatin Jihar Katsina da ta dauki matakin gaggawa kan hanyar.
Haka kuma, wata mata daga yankin, Fatima Abdullahi, ta koka kan yadda mummunan yanayin hanyar ke hana mazajensu fita neman abin dogaro da rayuwa.
Haka nan, wani tsohon jami’in lafiya a Jihar Katsina, Dr. Haruna Abubakar, ya bukaci Gwamnatin Jihar Katsina da ta saka aikin gina hanyar Tsangamawa, Babban Rafi a kasafin kudin bana saboda mahimmancinsa ga al’umma.
Matan yankin sun roki Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Dikko Umar Radda, da ya tausaya musu da iyalansu ta hanyar gyara hanyar.
Duk da cewa hanyar tana da kimanin kilomita 23 kacal, gwamnatocin baya sun kasa gyarata. Dole ne gwamnati ta fara fifita yankunan karkara wajen bayar da kwangiloli domin inganta rayuwar al’umma.
Cov/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jariransu
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
Kwanaki takwas bayan wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye garin Mokwa, hedikwatar Ƙaramar hukumar Mokwa a Jihar Neja, an gano gawar mutum ɗaya daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, an tsinci gawar ne a ranar Alhamis a wata gona da ke kan hanyar wucewa kusa da wani wuri da aka fi sani da ‘dam’.
Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiA cewar shaidun gani da ido, an kasa tantance wanda abin ya shafa saboda gawar ta lalace. An binne shi ne a inda aka gano gawarsa.
Wata mazauniyar yankin mai suna Tswata Mai Rubutu da ta zanta da Aminiya ta wayar tarho, ta ce an tsinci gawar a kan hanyar da ruwa ke wucewa.
“Gawar wani babban mutum ne, amma ba za mu iya gane shi ba saboda tuni ya fara lalacewa. An binne shi a wurin tun da ba a iya motsa gawar,” in ji shi.
An yi ƙoƙarin jin ta bakin Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullahi Baba Arah, domin ƙarin bayani lamarin ya ci tura.
Tun da farko hukumar ta tabbatar da mutuwar mutane 161, yayin da wasu da dama suka ɓace bayan iftila’in ambaliyar.