Gwamnatin tarayya ta ce za ta hada gwiwa da gwamnatin jihar Jigawa wajen bunkasa kiwon dabbobi domin dorewar samar da abinci da ci gaban tattalin arzikin kasar nan.

Ministan kula da ci gaban harkokin dabbobi Alhaji Idi Mukhtar Maiha ya bayyana haka, a lokacin da ya karbi bakuncin gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi a ma’aikatarsa da ke Abuja.

Ya yi nuni da cewa, wani bangare na shirin shi ne kafa jami’an hadin gwiwa don gano wuraren da za a ba da fifiko da kuma samar da manufofin da za a iya aiwatarwa cikin gaggawa.

Da yake yabawa jihar Jigawa bisa manufofinta na kiwo, ministan ya ce tsarin da gwamnatin jihar ta bullo da shi na bunkasa kiwon dabbobi abin koyi ne da ya kamata sauran jihohi su bi sahu.

“Mun gudanar da kididdiga a kasa baki daya game da abubuwan da suka shafi kiwo a fadin, wadanda suka hada da wuraren kiwo, hanyoyin shanu, da ruwa da ake da shi ta hanyar madatsun ruwa, da kasuwannin kiwo a fadin kasar nan.

“Muna farin ciki da ci gaban da aka samu a jihar Jigawa.”

“Tsarin samar da zaman lafiya a jihar Jigawa a yau abin koyi ne da zan ba da shawarar sauran jihohi su koya.

“Na san jihar Jigawa ta kasance daya daga cikin yankunan da suka fi fama da matsalar manoma da makiyaya.

“Na yaba da yadda jihar take bin tsarin samar da zaman lafiya na gargajiya da muka gada a baya, a yau, babu wani makiyayi da zai shiga kowace karamar hukumar Jigawa ba tare da karbar izini ba.”Inji Ministan.

Tun da farko a jawabinsa,
Gwamna Mallam Umar Namadi, ya bayyana bangarorin hadin gwiwa tsakanin gwamnatin tarayya da na jihar Jigawa da suka hada da dabarun karfafa saka hannun jari a harkar kiwon dabbobi, da shata hanyoyin da dabbobi ke bi domin magance rikicin manoma da makiyaya, da sauransu.

Ya kuma jaddada mahimmancin hadin gwiwa mai karfi tsakanin gwamnatocin jihohi da ma’aikatar tarayya, domin ganin an samar da hanyoyin da ba za a iya amfana da sana’ar kiwo a Najeriya, inda ya bayyana cewa fannin na da matukar muhimmanci wajen inganta samar da abinci, da ayyukan yi, da bunkasa tattalin arzikin kasa.

“Mun zo nan ne domin tayaka murnar wannanmatsayi da ka samu, kun zo a daidai lokacin da aka mutukar bukatar irin wannan ma’aikatar a kasar nan.

“Wannan ma’aikatar na da matukar muhimmanci, musamman wajen tafiyar da ajandar farfado da ci gaban kasa ta  mai girma shugaban kasa, ta fuskar samar da abinci da ci gaban tattalin arzikin kasar nan”

Gwamna Namadi ya ce “Mu a jihar Jigawa mun riga mun tsunduma cikin wannan fanni domin noma na cikin ajandarmu guda 12, inda aka bada fifiko  wajen bunkasa kiwon dabbobi”.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Jigawa a jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

 

Har ila yau, Lin ya ce matsayin kasar Sin dangane da rikicin kasar Ukraine bai sauya ba, cewa tattaunawa, da gudanar da shawarwari ne kadai hanyoyi mafiya dacewa na warware rikicin. Har kullum Sin na kan turbar adalci game da rikicin, tana kuma ci gaba da ingiza bukatar komawa teburin shawara tun barkewar rikicin. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar