Gwamnatin tarayya ta ce za ta hada gwiwa da gwamnatin jihar Jigawa wajen bunkasa kiwon dabbobi domin dorewar samar da abinci da ci gaban tattalin arzikin kasar nan.

Ministan kula da ci gaban harkokin dabbobi Alhaji Idi Mukhtar Maiha ya bayyana haka, a lokacin da ya karbi bakuncin gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi a ma’aikatarsa da ke Abuja.

Ya yi nuni da cewa, wani bangare na shirin shi ne kafa jami’an hadin gwiwa don gano wuraren da za a ba da fifiko da kuma samar da manufofin da za a iya aiwatarwa cikin gaggawa.

Da yake yabawa jihar Jigawa bisa manufofinta na kiwo, ministan ya ce tsarin da gwamnatin jihar ta bullo da shi na bunkasa kiwon dabbobi abin koyi ne da ya kamata sauran jihohi su bi sahu.

“Mun gudanar da kididdiga a kasa baki daya game da abubuwan da suka shafi kiwo a fadin, wadanda suka hada da wuraren kiwo, hanyoyin shanu, da ruwa da ake da shi ta hanyar madatsun ruwa, da kasuwannin kiwo a fadin kasar nan.

“Muna farin ciki da ci gaban da aka samu a jihar Jigawa.”

“Tsarin samar da zaman lafiya a jihar Jigawa a yau abin koyi ne da zan ba da shawarar sauran jihohi su koya.

“Na san jihar Jigawa ta kasance daya daga cikin yankunan da suka fi fama da matsalar manoma da makiyaya.

“Na yaba da yadda jihar take bin tsarin samar da zaman lafiya na gargajiya da muka gada a baya, a yau, babu wani makiyayi da zai shiga kowace karamar hukumar Jigawa ba tare da karbar izini ba.”Inji Ministan.

Tun da farko a jawabinsa,
Gwamna Mallam Umar Namadi, ya bayyana bangarorin hadin gwiwa tsakanin gwamnatin tarayya da na jihar Jigawa da suka hada da dabarun karfafa saka hannun jari a harkar kiwon dabbobi, da shata hanyoyin da dabbobi ke bi domin magance rikicin manoma da makiyaya, da sauransu.

Ya kuma jaddada mahimmancin hadin gwiwa mai karfi tsakanin gwamnatocin jihohi da ma’aikatar tarayya, domin ganin an samar da hanyoyin da ba za a iya amfana da sana’ar kiwo a Najeriya, inda ya bayyana cewa fannin na da matukar muhimmanci wajen inganta samar da abinci, da ayyukan yi, da bunkasa tattalin arzikin kasa.

“Mun zo nan ne domin tayaka murnar wannanmatsayi da ka samu, kun zo a daidai lokacin da aka mutukar bukatar irin wannan ma’aikatar a kasar nan.

“Wannan ma’aikatar na da matukar muhimmanci, musamman wajen tafiyar da ajandar farfado da ci gaban kasa ta  mai girma shugaban kasa, ta fuskar samar da abinci da ci gaban tattalin arzikin kasar nan”

Gwamna Namadi ya ce “Mu a jihar Jigawa mun riga mun tsunduma cikin wannan fanni domin noma na cikin ajandarmu guda 12, inda aka bada fifiko  wajen bunkasa kiwon dabbobi”.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Jigawa a jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 

“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.

 

“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”

 

Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya