Kasar New Zealand Ta Gabatar Da Sabbin Sharuddan Barin Yahudawan Sahyoniya Shiga Kasar
Published: 28th, January 2025 GMT
Gwamnatin kasar News Zealand ta fitar da sabbin sharudda ga yahudawan HKI masu neman Visar Shiga kasar, daga ciki sai sun bada tarihin aikin sojen da suka yi a cikin kasarsu.
Takaita irin yahudawan da zasu shiga kasashen duniya bayana yakin Gaza dai, zai sanya wani tunani a zukatan yahudawan HKI musamman wadanda suka shiga yakin Gaza suka kuma yi wa Falasdinawa kissan kare dangi.
Kungiyoyi masu goyon bayan falasdinawa kimani 50 ne suka shigar da kara suka korafin a kissan kiyashe a Gaza wanda sojojin HKI suka yi a cikin watanni 15 da suka gabata a kotuna daban daban a duniya.
Gwamnatin kasar New Zealand dai tana tunanin hana duk wani soja daga cikin sojojin HKI wanda ya aikata kisan kiyashi a Gaza shiga kasarta. Ya zuwa yanzu dai gwamnatin kasar New Zealan ta haka akalla soja guda daga cikin sojojin HKI saboda kasancewa cikin sojojin da suka yi yaki a Gaza.
Jaridar Haaretz ta HKI ta bayyana cewa an sami irin wadannan korafe korafen a gaban kotuna a kasashen Afirka da Kudu, Sri Lanka, Belgium, Faransa, da kuma Brazil.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
A cewarsa, dukkanin takardar neman kirkirar sabon masarauta ko sarki ko gunduma dole ne a aike zuwa addireshin gwamnan jihar ta hannun babbar sakatariyar ma’aikatar kananan hukumomi da kula da masarautu na jihar.
Kazalika, ya ce dole ne masu nema su gabatar da takaitaccen tarihin al’ummar da suke nema wa masarauta ko sarki ko gudunmawa tare da tarihin masarautar ko sarki ko gundumar da ke yankin da suke neman fita daga ciki.
Sanarwar ta kuma nemi a sanya dukkanin wani muhimmin bayanin da aka san zai iya taimakawa wajen la’akari da bukatar masu nema.
Har ila yau, sanarwar ta ce dole ne a takardar neman a samu sahihin sanya hannun hakimi, sarakunam kauye, da shugabannin al’umma tare da tabbacin wannan neman ta fito ne daga al’ummar wannan yankin da ake nema mata masarauta ko sarki ko gunduma.
Sanarwar ta kara da cewa duk al’ummomin da ke son kirkirar sabbin masarautu, sarakuna, ko gundumomi su na da dama kuma su na da ‘yancin gabatar da bukatar neman.
Gidado ya jaddada cewa shirin na daya daga cikin kudirin gwamnati na bunkasa gudanar da harkokin kananan hukumomi, da kiyaye al’adu, da karfafa cibiyoyin gargajiya a matsayin muhimman ginshikan zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba masu ma’ana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp