Aminiya:
2025-09-18@00:43:00 GMT

2027: Malamai sun gudanar da addu’o’in nasarar Tinubu-Barau a Kano

Published: 11th, September 2025 GMT

Don tunkarar zaɓen 2027, wata Ƙungiya a ƙarƙashin inuwar Tinubu/Barau/Atah Movement a ranar Alhamis a Kano ta shirya taron addu’o’i na musamman domin samun nasara ga shugaban Ƙasa Bola Tinubu da Sanata Barau Jibrin.

Taron addu’ar wanda ya samu halartar Malaman addinin Musulunci da magoya bayan jam’iyyar APC daga Ƙananan hukumomin Jihar 44, an gudanar da shi ne a Gidan Baballiya Kurna da ke Ƙaramar hukumar Fagge.

Likitoci sun yi barazanar sake tsunduma yajin aiki An saki fursunonin siyasa 52 a Belarus

A yayin taron addu’o’in  malaman sun kammala karatun Alkur’ani mai girma tare da gabatar da addu’o’i na musamman kan takarar Tinubu a wa’adi na biyu da kuma burin Barau ya zama Gwamna a 2027.

Malaman sun kuma yi addu’ar Allah Ya ƙara wa ƙasar nan zaman lafiya, bunƙasar tattalin arziki, ci gaban ƙasa da kwanciyar hankali a siyasance.

Da yake zantawa da manema labarai, ɗaya daga cikin waɗanda suka shirya taron, Seyi Olorunshaya, ya ce an gudanar da taron ne domin marawa Tinubu baya da kuma yunƙurin Sanata Barau Jibrin na zama Gwamnan Jihar Kano.

“Shugaba Tinubu ya yi ƙoƙari cikin shekaru biyu kacal na mulkinsa, dubi ayyukan hanyoyi, farashin abinci da ke ci gaba da faɗuwa, samar da ayyukan yi da kuma ƙoƙarinsa kan tsaro,” in ji Olorunshaya.

“A cikin ’yan shekarun da suka gabata, ’yan Najeriya da a baya suka yi ta kuka a kullum kan rashin tsaro, tsadar kayayyaki da sauran kayayyaki, yanzu sun fara ganin sauyi na gaske tare da alamun samun mafita mai kyau.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Barau I Jibirin

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
  •   Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam ” Nahid 2″ Da Zai Samar Wa Yankunan Karkara Hanyar Sadarwa Ta “Internet”
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago