Trump ya tiso ƙeyar rukunin farko na ’yan Najeriya daga Amurka
Published: 11th, September 2025 GMT
Rukunin farko na ’yan Najeriya da aka tsara korar su daga Amurka a karkashin Shugaba Donald Trump sun bar kasar.
Shugaban Ghana, John Dramani Mahama, ne ya bayyana hakan ga ’yan jarida a daren Laraba.
“Rukunin mutane 14 da aka kora daga Amurka, ciki har da ’yan Najeriya da wani dan kasar Gambiya, sun iso Ghana, kuma gwamnati ta taimaka wajen mayar da su kasashensu,” in ji Mahama a wani taron manema labarai.
Ya ce Ghana ta riga ta shirya jigilar ’yan Najeriya zuwa kasarsu ta mota, yayin da ake ci gaba da taimaka wa dan Gambiya don shi ma ya koma kasar shi.
“Amurka ta tuntube mu don mu karbi ’yan kasashen waje da ba ’yan Ghana ba da za a fitar daga Amurka. Mun amince da cewa za mu karbi ’yan kasashen Yammacin Afirka,” in ji Mahama.
“Duk ’yan Yammacin Afirka ba sa bukatar takardar izinin shiga Ghana.”
Gwamnatin Trump dai a baya ta tuntubi kasashen Afirka da dama don su karbi ’yan kasashensu da aka kora daga Amurka a wani yunkuri na rage kwararar bakin haure.
Wasu daga cikin wadanda aka fitar dai ’yan kasashen Jamaica, Vietnam da Laos ne, inda kungiyoyin kare hakkin bil’adama ke cewa hakan ya saba wa hakkinsu na asali.
Wasu kasashen sun nuna adawa da wannan tsarin na korar baki.
Najeriya, wadda ta sha bayyana matsayinta, ta ce ba za ta yarda da matsin lamba daga Amurka don karbar ’yan kasashen waje da ba ’yan Najeriya ba.
A watan Yuli, Amurka ta fitar da mutane biyar zuwa Eswatini da wasu takwas zuwa Sudan ta Kudu.
Rwanda ma ta karbi ’yan gudun hijira bakwai da aka kora daga Amurka a watan Agusta, bayan da kasashen biyu suka cimma yarjejeniya don karbar har mutane 250.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan Najeriya yan kasashen
এছাড়াও পড়ুন:
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
Dan wasan da ya lashe kyautar a bara, Ademola Lookman na Nijeriya ba ya cikin jerin ‘yan wasan da aka lissafo a bana, inda hukumar kwallon kafa ta Afirka (Caf) ta samar da kwamitin kwararru wanda ya zakulo masu horarwa da ‘yan wasan da suka “Taka rawar gani” a tsakanin 6 ga watan Janairu zuwa 15 ga watan Oktoban wannan shekara.
An bayyana sunan mai horar da tawagar ‘yan kwallon kafa ta kasar Cape Berde, Bubista a matsayin mai neman lashe kyautar mai horarwa mafi kwazo bayan jagorantar tawagar kasar ta Blue Sharks wajen samnun gurbin gasar kofin duniya a karon farko a tarihi.
Haka nan tawagar ta tsibirin Cape Berde na cikin masu gogayyar lashe kungiya mafi hazaka a shekarar, tare da Morocco wadda a baya-bayan nan ta lashe kofin duniya na gasar kwallon kafa ta ‘yan kasa da shekara 20.
‘Yanwasa mata na Nijeriya Esther Okoronkwo da Rasheedat Ajibade na cikin wadanda ke neman lashe kyautar zakarun ‘yanwasa mata na Afirka na wannan shekarar. Ya zuwa yanzu dai hukumar CAF ba ta bayyana ranar da za a yi bikin bayar da kyautar ba.
Dan wasa mafi Kwazo: Andre-Frank Zambo Anguissa (Napoli da Kamaru), Denis Bouanga (Los Angeles FC da Gabon), Serhou Guirassy (Borussia Dortmund da Guinea), Achraf Hakimi (Paris St-Germain da Moroko), Oussama Lamlioui (Renaissance Berkane), Fiston Mayele (Pyramids da DR Congo), Iliman Ndiaye (Eberton da Senegal), Bictor Osimhen (Galatasaray da
Nigeria), Mohamed Salah (Liberpool da Masar), Pape Matar Sarr (Tottenham Hotspur da Senegal).
Mai tsaron raga na maza: Yassine Bounou (Al Hilal da Moroko), Aymen Dahmen (CS Sfadien da Tunisia), Marc Diouf (TP Mazembe da Senegal), Edouard Mendy (Al-Ahli da Senegal), Munir Mohamedi (RS Berkane da Moroko), Stanley Nwabali (Chippa Utd da Nijeriya), Andre Onana
(Trabzonspor da Kamaru), Ahmed El Shenawy (Pyramids da Masar), Bozinha (Chabes da Cape Berde), Ronwen Williams (Mamelodi Sundowns da Afirka ta Kudu).
Mai horar da kungiyar maza: Bubista (Cape Berde), Moine Chaabani (Renaissance Berkane), Hossam Hassan (Masar), Krunoslab Jurcic (Pyramids), Mohamed Ouahbi (Moroko U20), Romuald Rakotondrabe (Madagascar), Walid Regragui (Moroko), Tarik Sektioui (Moroko U23), Pape Thiaw (Senegal), Sami Trabelsi (Tunisia).
Tawagar maza: Algeria, Cape Berde, Masar, Ghana, Ibory Coast, Moroko, Moroko U20, Senegal, Afirka ta Kudu, Tunisia. ‘Yan wasa Mata da ke takarar lashe zakarun Afirka na shekara ta 2025.
‘Yar wasa mafi kwazo: Rasheedat Ajibade (Paris St-Germain da Nijeriya), Barbra Banda (Orlando Pride da Zambia), Portia Boakye (Hapoel Petah Tikba da Ghana), Tabitha Chawinga (Lyon da Malawi), Temwa Chawinga (Kansas City da Malawi), Ghizlaine Chebbak (Al Hilal da Moroko), Mama Diop (Strasbourg da Senegal), Rachael Kundananji (Bay FC da Zambia),
Sanaa Mssoudy (AS FAR da Moroko), Esther Okoronkwo (AFC Toronto da
Nijeriya).
Mai tsaron raga na mace: Sedilame Boseja (Mamelodi Sundowns da Botswana), Andile Dlamini (Mamelodi Sundowns da Afirka ta Kudu), Habiba Emad (FC Masar da Masar), Khadija Er-Rmichi (AS FAR da Moroko), Fatoumata Karantao (MUSFAS Bamako da Mali), Cynthia Konlan (Swieki United da Ghana), Adji Ndiaye (AS Bambey da Senegal), Fideline Ndoy (TP
Mazembe da DR Congo), Chloe N’Gazi (Marseille da Algeria), Chiamaka Nnadozie (Brighton & Hobe Albion da Nijeriya).
Mai horar da kungiyar mata: Genobeba Anonman (15 de Agosto), Kim Bjorkegren (Ghana), Lamia Boumehdi (TP Mazembe), Desiree Ellis (Afirka ta Kudu), Carol Kanyemba (Zambia U17), Adelaide Koudougnon (Ibory Coast U17), Justin Madugu (Nijeriya), Bankole Olowookere (Nijeriya U17), Siaka Gigi Traore (ASEC Mimosas), Jorge Bilda (Moroko).
Tawagar mata: Kamaru U17, Ghana, Ibory Coast U17, Mali, Morocco, Nijeriya, Nijeriya U17, Afirka ta Kudu, Tanzania, Zambia U17. Za ku iya ganin cikakken jerin wadanda ke neman lashe kyautukan a shafin hukuma Caf. [1]
ShareTweetSendShare MASU ALAKA