’Yan bindiga da masu ɗaukar musu bayanai ba su da bambanci — Gwamnan Sakkwato
Published: 9th, September 2025 GMT
Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya buƙaci jami’an tsaro da su riƙa ɗaukar duk wani infoma da ke bayar da bayani ga ’yan bindiga a matsayin abu ɗaya da babu wani bambanci a tsakaninsu.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyara ƙananan hukumomin Wurno da Rabah a ranar Litinin da ta gabata, domin jajanta wa al’umma bisa hare-haren da ’yan bindiga ke kai musu.
Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen daƙile matsalar ’yan bindiga a faɗin jihar, inda ya buƙaci mazauna ƙauyuka su riƙa tona asirin duk wanda suka sani yana bai wa ’yan bindiga bayanai, domin hukuma ta ɗauki matakin da ya dace.
Gwamnan ya bayyana irin takaicin da yake ji kan masu kai kai wa ’yan ta’adda bayanai saboda ɗan wani abin da bai taka kara ya karya ba, yana mai cewa hakan rashin kishin ƙasa ne.
Ya kuma gargaɗi duk masu wannan mummunar ɗabi’a cewa ba za su tsira ba a sakamakon wannan sabon tsarin da gwamnatin sa ta fito da shi na kawar da ’yan bindiga daga jihar.
“Mun himmatu don ganin mun zaƙulo waɗannan infoma da suka hana jama’armu zaman lafiya ko ta halin ƙaƙa.
“Don haka muke roƙon jama’a da su bayar da haɗin kai don dawo da zaman lafiya mai ɗorewa a Jihar Sakkwato,” in ji gwamna Ahmad.
Gwamnan ya kuma buƙaci limaman Juma’a da sauran malamai da su yi wa’azi a kan irin laifin da ke cikin taimaka wa ’yan bindiga, da matsayin addini kan irin waɗannan ayyukan ɓarna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Sakkwato yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
Wani sojan Ƙasar Amurka ɗan asalin Jihar Kano, Suleiman Isah, wanda yake aiki a rundunar sojin Amurka, ya ce ba zai yaƙi da ƙasarsa ta haihuwa ba saboda yaɗa labaran ƙarya game da yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.
Isah, wanda ya shiga rundunar sojin Amurka shekaru biyu da suka gabata, yana aiki ne da rundunar California Army National Guard, mai dakaru sama da 18,000.
Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin AmurkaA wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook wanda Aminiya ta tabbatar, Isah ya mayar da martani kan jita-jitar cewa Amurka za ta ɗauki matakin yaƙi a kan Najeriya saboda zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.
Ya bayyana cewa ba zai taɓa amfani da makami a kan mutanensa ba.
“Ba zan shiga Najeriya na kashe iyayena ba saboda ƙaryar cewa ana kashe Kiristoci,” in ji shi.
Ya ce duk da yake yana Allah-wadai da kashe-kashe da tashin hankali, bai kamata matsalar tsaro a Najeriya a danganta da wani addini ba.
“Ba zan ƙaryata batun kisan Kiristoci da Musulmai ba,” in ji shi.
“Shekau, Bello Turji, Dogo Gide da sauransu ba suna kai wa wani addini ɗaya hari ba ne kaɗai.”
Maganganun Isah na zuwa ne daidai lokacin Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi a kan Najeriya.
Sai dai Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini ba ce, inda ta ce matsalar na shafar Musulmai da Kiristoci baki ɗaya.