Aminiya:
2025-11-02@12:30:13 GMT

Yarima Harry ya ziyarci kabarin Sarauniya Elizabeth II

Published: 8th, September 2025 GMT

Yarima Harry wanda ya koma rayuwa a Jihar California ta Amurka, ya ziyarci kabarin mahaifiyarsa, Sarauniya Elizabeth II, a fadar Windsor da ke yammacin birnin Landan a ranar Litinin.

Shekaru uku ke nan daidai da rasuwar Sarauniya Elizabeth II wadda ta riga mu gidan gaskiya a ranar 8 ga Satumba, 2022, kuma aka binne ta a cikin cocin St.

George’s Chapel da ke fadar Windsor.

An fara samun masu zawarcin kujerar Firaministan Japan Matatar Dangote ta musanta dakatar da aiki

Mai magana da yawunsa ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa Harry ya kai ziyara shi kaɗai domin girmama mahaifiyarsa.

A halin yanzu dai abin tambayar shi ne ko Yarima Harry zai gana da mahaifinsa, Sarki Charles III, wanda ke fama da cutar daji, bayan shekaru suna fama da rigimar cikin gida.

Rabon Harry ya gana da mahaifinsa tun watan Fabrairu 2024, lokacin da ya yi gaggawar dawowa Ingila bayan ya samu labarin cewa sarkin mai shekara 76 na fama da jinya.

Yarima Harry, mai shekara 40, ya halarci bikin ba da kyaututtuka na WellChild a daren Litinin a birnin London, inda ake girmama jarirai da yaran da suka yi bajinta duk da nakasa ko rashin lafiya.

Hotunan ziyarar da Yarima Harry ya kai taron ba da kyaututtuka na Well Child

Bayan haka kuma, ana sa ran zai tafi Nottingham a Arewacin Ingila a ranar Talata domin ziyartar wani gidan rikodin al’umma da kuma sanar da tallafin kuɗi a shirin Children in Need, wata ƙungiya da ke fafutukar taimaka wa yaran da ke cikin mawuyacin hali.

Tun daga shekarar 2020 Harry ya daina shiga harkokin gidan sarauta kai tsaye, lamarin da ya jawo cece-kuce, musamman tsakaninsa da ɗan uwansa Yarima William, wanda shi ne mai jiran gado.

A watan Mayu, Yarima Harry ya bayyana cewa yana fatan a samu sulhu tsakaninsa da ’yan uwansa, yana mai cewa: “Ban san adadin kwanakin da suka rage wa mahaifina a duniya ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sarauniya Elizabeth II Sarauniyar Ingila Sarki Charles III

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi

Gwamnatin Amurka ƙarƙashin Donald Trump ta sake sanya Najeriya cikin jerin “Ƙasashe Masu Matsala ta Musamman” saboda zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Wannan zargi ya biyo bayan jawabin da Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya yi a taron Majalisar Ɗinkin Duniya a kwanan baya.

Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP

A lokacin taron Shettima ya bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin abin tausayawa, inda ya hi kira da a tabbatar da zaman lafiya ta hanyar kafa ƙasashe biyu masu zaman kansu.

Bayan jawabin nasa, wasu ƙungiyoyi suka fara yaɗa labarin cewa ana yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Najeriya, duk da cewa mutane da dama sun ƙaryata jita-jitar.

A ranar Juma’a, Trump ya wallafa wani rubutu a shafinsa na X, cewa Kiristoci na fuskantar barazana a Najeriya.

Ya yi iƙirarin cewar masu tsattsauran ra’ayi suna yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya .

Ya umarci ɗan Majalisar Amurka, Riley Moore da shugaban kwamitin kasafin kuɗi na Majalisar, Tom Cole, su binciki lamarin, sannan su gabatar masa da rahoto.

Shugaban ya ƙara da cewa ƙasarsa ba za ta zuba ido yayin da irin wannan “ta’addanci” ke faruwa a Najeriya da sauran ƙasashe ba.

Ya lashi takobin cewar Amurka za ta ci gaba da kare Kiristoci a duniya baki ɗaya.

Bayan wannan furuci, wasu sun zargi Trump da amfani da matsalar tsaron Najeriya don samun goyon bayan siyasa.

Har yanzu Gwamnatin Najeriya ba ta yi martani a kan lamarin ba, amma jami’an gwamnati a baya sun bayyana cewa rikice-rikicen da ake fama da su a ƙasar suna da nasaba da ayyukan ta’addanci, fashi, da rikicin ƙabilanci, ba addini ba.

Kalmar “Ƙasa Mai Matsala Ta Musamman” na nufin ƙasashen da Amurka ke ganin suna take haƙƙin ’yancin addini, kuma hakan na iya sa wa ta ƙaƙaba wa Najeriya takunkumai.

Idan ba a manta Najeriya ta fara shiga jerin irin waɗanda ƙasashe tun a shekarar 2020.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa