Aminiya:
2025-09-18@00:44:36 GMT

Yarima Harry ya ziyarci kabarin Sarauniya Elizabeth II

Published: 8th, September 2025 GMT

Yarima Harry wanda ya koma rayuwa a Jihar California ta Amurka, ya ziyarci kabarin mahaifiyarsa, Sarauniya Elizabeth II, a fadar Windsor da ke yammacin birnin Landan a ranar Litinin.

Shekaru uku ke nan daidai da rasuwar Sarauniya Elizabeth II wadda ta riga mu gidan gaskiya a ranar 8 ga Satumba, 2022, kuma aka binne ta a cikin cocin St.

George’s Chapel da ke fadar Windsor.

An fara samun masu zawarcin kujerar Firaministan Japan Matatar Dangote ta musanta dakatar da aiki

Mai magana da yawunsa ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa Harry ya kai ziyara shi kaɗai domin girmama mahaifiyarsa.

A halin yanzu dai abin tambayar shi ne ko Yarima Harry zai gana da mahaifinsa, Sarki Charles III, wanda ke fama da cutar daji, bayan shekaru suna fama da rigimar cikin gida.

Rabon Harry ya gana da mahaifinsa tun watan Fabrairu 2024, lokacin da ya yi gaggawar dawowa Ingila bayan ya samu labarin cewa sarkin mai shekara 76 na fama da jinya.

Yarima Harry, mai shekara 40, ya halarci bikin ba da kyaututtuka na WellChild a daren Litinin a birnin London, inda ake girmama jarirai da yaran da suka yi bajinta duk da nakasa ko rashin lafiya.

Hotunan ziyarar da Yarima Harry ya kai taron ba da kyaututtuka na Well Child

Bayan haka kuma, ana sa ran zai tafi Nottingham a Arewacin Ingila a ranar Talata domin ziyartar wani gidan rikodin al’umma da kuma sanar da tallafin kuɗi a shirin Children in Need, wata ƙungiya da ke fafutukar taimaka wa yaran da ke cikin mawuyacin hali.

Tun daga shekarar 2020 Harry ya daina shiga harkokin gidan sarauta kai tsaye, lamarin da ya jawo cece-kuce, musamman tsakaninsa da ɗan uwansa Yarima William, wanda shi ne mai jiran gado.

A watan Mayu, Yarima Harry ya bayyana cewa yana fatan a samu sulhu tsakaninsa da ’yan uwansa, yana mai cewa: “Ban san adadin kwanakin da suka rage wa mahaifina a duniya ba.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sarauniya Elizabeth II Sarauniyar Ingila Sarki Charles III

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa