Aminiya:
2025-11-02@17:02:16 GMT

DSS ta bai wa shafin X wa’adin goge saƙon Sowore da ke ƙaryata Tinubu

Published: 7th, September 2025 GMT

Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya (DSS) ta bai wa shafin sada zumunta na X wa’adin sa’o’i 24 da ya goge wani saƙo da mai fafatuka Omoyele Sowore ya wallafa yana ƙaryata Shugaba Bola Tinubu.

Hakan na ƙunshe cikin wata wasiƙa da Hukumar DSS ɗin ta aike wa kamfanin X Corp mallakin fitaccen attajirin nan Elon Musk.

Firaministan Japan Shigeru Ishiba ya yi murabus ’Yan ta’adda sun kashe mutum 63 a Borno

A wasiƙar da DSS ta wallafa shafinta na X ranar Asabar, hukumar ta zargi Mista Sowore da yin amfani da saƙonsa na X wajen cin fuskar shugaban ƙasa Tinubu da yi masa rashin mutunci da ba’a.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ranar 25 ga watan Agusta, Mista Sowore ya soki ziyarar da shugaban Nijeriya ya kai Brazil da kuma kalaman da shugaban ya yi yayin ziyarar.

“Mai laifi @officialABAT [Bola Tinubu] ya kai ziyara Brazil inda ya ce babu cin hanci da rashawa a Nijeriya a gwamnatinsa. Ji wani ƙarfin hali na ƙarya da ko kunya babu!” in ji Omoyele Sowore (@YeleSowore) ranar 26 ga watan Agustan shekarar 2025.

A cikin wasiƙar da DSS ta aike wa kamfanin X ta ce waɗannan kalaman sun ɓata wa magoya bayan Shugaba Tinubu rai, lamarin da ya sa suka yi zanga-zangar rashin amincewa da kalaman na Sowore a kan titunan ƙasar.

Saboda haka, hukumar ta bai wa shafin X wa’adin sa’o’i 24 domin ya cire kalaman Sowore ko kuma ta ɗauki matakai masu tsauri a kan shafin.

Abin da Tinubu ya ce a Brazil

Ana iya tuna cewa dai a yayin ziyarar da Shugaba Tinubu ya kai ƙasar Brazil a watan jiya, ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatinsa ta yi a Nijeriya sun kawo ƙarshen cin hanci a ƙasar.

“Sauyen-sauyen da na ƙaddamar tun da na karɓi ragamar mulki a Nijeriya suna tasiri sosai. Zan iya bugun ƙirji kan haka. Daga farko sun ba da wahala. Amma a yau sakamakonsu yana haɓaka,” in ji Shugaba Tinubu.

“Yana daɗa bayyana ga mutane. Mun ƙara yawan kuɗi cikin tattalin arzikinmu. Yanzu babu cin hanci da rashawa. Gwamnan babban bankin [Nijeriya] ya zo nan. Ba sai ka san shi ba kafin ka samu takardun kuɗin ƙasashen waje da kake buƙata,” in ji shi.

Martanin Sowore

Shi kuwa mai fafatuka, Omoyele Sowore, wanda hukumar DSS take ƙorafi game da saƙon da ya wallafa ya mayar da martani da saƙon DSS.

“Da safiyar yau, X (wanda a baya ake kira Twitter) ya tuntuɓe ni a hukumance game da wasiƙar barazana da suka samu daga hukumar DSS mara bin doka game da saƙon da na wallafa kan Tinubu. Ba zan goge saƙon ba,” in ji Sowore a saƙonsa na X.

Sai dai a halin yanzu abin jira a gani shi ne abin da zai biyo bayan wa’adin sa’o’i 24 da hukumar DSS ta bai wa X.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hukumar DSS

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Trump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”

A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.

“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”

Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.

“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.

Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu