Aminiya:
2025-09-18@00:42:59 GMT

Gwamnatin Sakkwato ta ba jami’an tsaro tallafin motoci 14 da babura 150

Published: 5th, September 2025 GMT

Gwamnatin jihar Sakkwato ta bayar tallafin motoci 14 kirar Hilux da babura 150 ga dukkan jami’an tsaron jihar don karfafa aikin sintiri.

Tallafin kari ne a kan Hilux 170 da babura da gwamnatin ta bayar a baya.

Ba abin mamaki ba ne idan na fice daga NNPP – Abdulmumin Kofa ’Yan sandan Kaduna sun gayyaci El-Rufa’i kan zargin yunkurin tayar da zaune tsaye

Sakataren Gwamnatin jihar, Muhammad Bello Sifawa ne ya miƙa kayan a madadin Gwamnan jihar, Ahmad Aliyu a wani ƙwarya-ƙwaryar bikin da aka yi a gidan gwamnatin jiha a ranar Alhamis.

Bello Sifawa ya ce hukumomin tsaro ne suka roki a ba su ababen hawan a lokacin zaman majalisar tsaro ta jihar, shi kuma Gwamnan ya amince

Ya nuna bukatar da ake da ita ga jami’an tsaron kan su yi amfani da motocin da baburan ga abin da ake son a yi domin kare dukiya da rayukan jama’a.

Hakan a cewar Sakataren na cikin babban kudurin gwamnatin.

Da yake jawabi a madadin dukkan jami’an tsaron, kwamishinan ’Yan Sanda na jiha Ahmad Musa ya gode wa gwamnatin jiha kan amincewa da rokon nasu cikin lokaci

Kwamishinan ya kuma gode wa gwamnatin kan hadin kai da take bai wa jami’an tsaro, tare da bayar da tabbacin yin amfani da ababen hawan domin karfafa tsaro a jihar.

Ahmad ya ba da tabbacin jami’an tsaro za su ci gaba da aiki ba dare ba rana don tabbatar da zaman lafiya da taron rayuwa da dukiyar al’umma, za su taimaki gwamnati don samun nasara.

Kwamishina ya yi kira ga mutane su rika ba da bayani duk wani bakon abu da suka gani a yankunan su da ba su amince da shi ba, domin inganta tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro Sakkwato jami an tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

An garzaya da shi zuwa babban Asibitin Gwamnatin Tarayya da ke Birnin Kebbi, inda daga bisani likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.

An yi jana’izarsa a babban masallacin Sarkin Gwandu, sannan aka binne shi a makabartar Dukku da ke kan hanyar Makera zuwa Kangiwa.

Jana’izar ta samu halartar jami’an kwas5tan, ‘yan uwa, abokai da sauran mu5sulmi daga sassa daban-daban na jihar.

Har yanzu al’ummar garin Filgila da kewaye na cikin tashin hankali da fargaba, kasancewar hare-haren Lakurawa na jefa su cikin zulumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin