Ɓarkewar cutar Ebola ta kashe mutum 15 a Congo
Published: 5th, September 2025 GMT
Mahukuntan lafiya sun tabbatar da sabuwar ɓarkewar cutar Ebola a Jamhuryar Dimokraɗiyyar Congo wadda zuwa ƙarshen watan Agustan da ya gabata ta yi ajalin mutum 15 a lardin Kasai da ke tsakiyar ƙasar.
Ministan Lafiya, Samuel Roger Kamba, ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai ranar Alhamis a Kinshasa, babban birnin ƙasar.
Rahotanni sun nuna cewa an samu mutum 28 da ake zargin sun kamu da cutar a lardin Kasai, inda a karon farko a ranar 20 ga watan Agusta aka gano ta a jikin wata mata mai juna biyu mai shekara 34 bayan kwantar da ita a asibiti.
“Wannan shi ne karo na 16 da aka samu ɓarkewar Ebola a ƙasarmu,” in ji Ministan Kamba.
Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce adadin masu cutar na iya ƙaruwa, inda ta riga ta tura ƙwararrunta tare da tawagar ƙungiyar agajin DRC zuwa lardin Kasai domin ba da gudummawar daƙile yaɗuwar cutar.
A cewar Darektan WHO na Afirka, Mohamed Janabi, akwai magungunan da aka tanada da allurai 2,000 na rigakafin cutar Ebola, waɗanda za a tura daga Kinshasa zuwa Kasai nan ba da jimawa ba.
Cutar Ebola, wacce aka fara gano ta a shekarar 1976 daga ɓerayen daji, cuta ce mai haɗari da ke yaɗuwa ta hanyar hulɗa da jini ko ruwa a jikin mai cutar.
Ɓarkewar cutar mafi muni a tarihin DRC ta faru ne tsakanin 2018 zuwa 2020, inda aka rasa rayukan fiye da mutum 2,300.
A yanzu haka, hukumomin lafiya sun tabbatar da cewa irin nau’in Zaire na Ebola ne ya sake ɓulla, wanda ake da rigakafi a kansa.
“Abin farin ciki shi ne akwai rigakafin nau’in Zaire, amma kafin a fara yi wa jama’a allurar, sai an kammala shirin tsara dabarun isar da ita,” in ji Ministan Lafiya Kamba.
Wannan ne karo na 16 da ake samun ɓarkewar cutar a ƙasar tun bayan da aka fara ganota kusan shekara 40 da suka gabata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jamhuriyyar Dimokradiyyar Congo cutar Ebola
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai
A jawabinsa yayin taron, Gwamna Sani ya gabatar da kasida mai taken: “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa”, inda ya bayyana yadda Jihar Kaduna ke ci gaba da samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma, da tsarin tallafiwa jama’a.
Gwamnan Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki da kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su samu nasara a rayuwarsu.
Gwamna Uba Sani, ya kuma halarci shirin baje koli na birnin Dubai mai taken : “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira, da Tasirin Zamantakewa”, inda nan ma ya jaddada cewa jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha a mulki suna da matuƙar muhimmanci wajen buɗe damarmaki ga mutane da birane.
A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da wata ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta Janar na birnin Dubai inda suka tattauna batutuwan haɗin gwiwa a fannin kirkirar makamashin sharar gida da kula da sharar gida ta zamani, da kuma tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.
A ganawar, duk Bangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin jihar Kaduna zuwa tattalin arzikin mai ɗorewa.
Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Jihar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun ƙasashen duniya wajen yin haɗin kai, ƙirƙira, da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa da ci gaban kowa da kowa a fadin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya
ShareTweetSendShare MASU ALAKA