Aminiya:
2025-11-02@21:10:43 GMT

Manchester United za ta ɗauki golan Antwerp, Senne Lammens

Published: 2nd, September 2025 GMT

Manchester United ta amince za ta ɗauki golan tawagar Belgium, Senne Lammens daga Royal Antwerp kan fam miliyan 18.1 har da karin tsarabe-tsarabe.

Sasashen wasanni na BBC ya ruwaito cewa hakan ya kawo karshen zawarcin golan Aston Villa, Emiliano Martinez da ta yi.

An kama uba da ɗansa kan yi wa ’yar shekara 13 fyaɗe a Gombe An kama ɗan shekara 60 kan yi wa mai shekara 24 fyaɗe

Lammens, mai shekara 23, zai saka hannu a ƙungiyar Old Trafford kan yarjejeniyar kaka biyar.

United na fatan ɗinke ɓarakar gurbin mai tsaron raga, bayan da Altay Bayindir ke kuskure a wasannin Firimiya, yayin da ake zargin Andre Onana da sakacin da ya janyo aka fitar da United a Carabao Cup a hannun Grimsby.

Lammens ya koma Antwerp a matakin mara ƙunshin yarjejeniya daga Club Brugge a 2023, wanda ya tsare raga karo 64 a Antwerp da lashe Belgian Super Cup a 2023.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Royal Antwerp

এছাড়াও পড়ুন:

Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe

Wani fursuna mai suna Abba Hassan, wanda aka yanke wa hukuncin kisa, ya tsere daga gidan gyaran hali na Potiskum da ke Jihar Yobe.

Rundunar ’yan sanda ta Jihar, ta tabbatar da wannan lamari a cikin wata sanarwa da kakakinta, DSP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Asabar.

Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka

A cewar sanarwar, Abba Hassan, wanda asalinsa ɗa  Jihar Borno ne, ya gudu daga gidan yarin a ranar 31 ga watan Oktoba, bayan kotu ta yanke masa hukuncin kisa.

DSP Abdulkarim, ya roƙi jami’an tsaro, direbobi, sarakunan gargajiya, ’yan banga da al’ummomin Jihar Yobe da maƙwabtan jihohi da su taimaka da bayanai da za su taimaka wajen sake kama shi.

Ya kuma gargaɗi jama’a da kada su kusanci fursunan da ya tsere, domin hakan na iya zama hatsari.

“Domin kare lafiyarku, idan kuka ga wani da kuke zargi shi ne, ku sanar da ofishin ’yan sanda mafi kusa ko gidan gyaran hali, ko kuma ku kira lambar 08038452982,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku