AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci
Published: 2nd, September 2025 GMT
Mukaddashin daraktan ofishin bunkasa tattalin arziki, hada kai da raya cinikayya a hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, mista Patrick Ndzana Olomo, ya ce nahiyar Afirka da Sin na da makoma mai haske a fannin raya hadin gwiwa, don bunkasa harkokin noma da shawo kan matsalar kamfar abinci a Afirka.
Olomo, wanda ya yi tsokacin a ranar Juma’a yayin da ya ziyarci cibiyar gwajin fasahohin noma, inda kwararrun kasar Sin ke baje kolin fasahohin zamani na inganta noma dake birnin Addis Ababa fadar mulkin kasar Habasha, ya ce kasashen Afirka da Sin na aiki tare wajen samar da gamammen tsarin bunkasa noma, wanda zai ingiza matsayin nahiyar Afirka zuwa ga cimma nasarar samar da isasshen hatsi da wadatuwar abinci.
Masaniyar aikin gona ta hukumar gudanarwar kungiyar AU Patience Mhuriro-Mashapa ita ma ta yabawa irin ci gaban da alakar sassan biyu ta samu zuwa mataki mafi muhimmanci a tarihi, ta kuma jinjinawa kwazon kasar Sin na aiki tare da bangaren Afirka, a fannin bunkasa fasahohin zamani na noma, inda ta ce kwararrun kasar Sin sun jima suka aiki tare da takwarorinsu na Afirka wajen gina sabbin tsare-tsaren raya noma, da gabatar da sabbin nau’o’in irin shuka, da inganta dabarun samar da yabanya mai yalwa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
An gudanar da taron tattaunawa na duniya kan kirkire-kirkire da bude kofa da ci gaba na bai daya, jiya Juma’a a birnin Lagos na Nijeriya. Yayin taron wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG da karamin ofishin jakadancin Sin dake Lagos suka shirya, ministan kula da harkokin matasa na Nijeriya Ayodele Olawande da shugaban CMG Shen Haixiong, sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo.
A cewar ministan na Nijeriya, cikin shekaru 5 da suka gabata, dubban matasan kasar sun ci gajiyar tallafin karatu da shirye-shiryen horo da na musaya da Sin ta samar, kuma wannan hadin gwiwa da ake yi a aikace ya kara fahimta da aminci tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, a shirye ma’aikatarsa take ta karfafa hadin gwiwa da sassa masu ruwa da tsaki na kasar Sin wajen ci gaba da fadada shirye-shiryen musaya da na hadin gwiwa da suka shafi matasa.
A nasa bangare, Shen Haixiong ya ce a matsayinta na babbar kafar yada labarai dake watsa shirye shiryenta ga sassa daban daban na duniya, tashar talabijin ta CCTV dake karkashin CMG da abokan huldarta, za su yayata shawarar Sin ta jagorantar harkokin duniya da gabatar da tafarkin Sin na zamanantar da kanta da karfinta na kirkire kirkire a sabon zamani ga al’ummar duniya. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA