Aminiya:
2025-11-02@17:09:40 GMT

Xi na karɓar baƙuncin taron SCO a China

Published: 31st, August 2025 GMT

Shugaban ƙasar China, Xi Jinping, na karɓar baƙuncin taron ƙungiyar Shanghai Cooperation Organisation (SCO) a birnin Tianjin, inda shugabannin ƙasashe kusan 20 daga yankin Eurasia suke halarta.

Taron, wanda zai gudana har zuwa Litinin, ana kallon sa a matsayin wani babban dandalin da ke ƙara tabbatar da matsayin China a tsakiyar harkokin siyasar ƙasashen Eurasia.

Gwamnonin Arewa Maso Gabas sun yi taro kan tsaro da tattalin arziƙi a Taraba Ambaliya: NEMA ta raba kayan tallafi a Yobe 

Shugaban Rasha, Vladimir Putin, ya isa Tianjin da manyan jami’an gwamnati da ’yan kasuwa daga ƙasarsa, inda kuma ya yi shirin gudanar da tattaunawa da shugabannin ƙasashe daban-daban a gefen taron.

Firayim Ministan Indiya, Narendra Modi, shi ma yana halartar taron, wanda ya kai ziyara ta farko zuwa China tun shekarar 2018.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin X, Modi ya ce: “Indiya za ta ci gaba da gina dangantaka da China bisa amincewa, mutuntawa da kuma fahimtar juna.”

Ya ƙara da cewa haɗin kan ƙasashen biyu zai amfanar da al’ummominsu da suka haura biliyan 2.8, tare da samar da ci gaba ga bil’adama gaba ɗaya.

Rahotanni sun nuna cewa tsohon rikicin iyaka tsakanin ƙasashen biyu da ya haddasa mutuwar sojoji a 2020, ya fara lafawa tun daga bara lokacin da shugabannin suka haɗu a wani taro a Rasha.

Daga cikin manyan shugabannin da suka halarci taron akwai shugaban ƙasar Belarus, Alexander Lukashenko, shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, da kuma shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, lamarin da ya sanya taron na bana zama mafi girma tun kafa ƙungiyar a 2001.

Masana sun bayyana cewa China da Rasha na amfani da SCO a matsayin wata hanya ta ƙarfafa tasirinsu a duniya a matsayin kishiyoyin ƙungiyoyin Yamma kamar NATO, musamman ganin yadda rikicin Ukraine da batun Taiwan ke jawo saɓani tsakaninsu da Turai da Amurka.

Bincike ya kuma nuna cewa Rasha na fatan amfani da SCO wajen samun goyon bayan ƙasashe masu tasowa, tare da ƙara kusantar Indiya a lokacin da take samun saɓani da Amurka kan batun shigo da mai daga Rasha.

Taron na Tianjin ya zo ne ’yan kwanaki kafin bikin gagarumin faretin soji da za a gudanar a birnin Beijing ranar Laraba, wanda zai ja hankalin shugabanni da dama daga sassa daban-daban na duniya, ciki har da Shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong Un.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Belarus Indiya Iran Koriya ta Arewa Kyrgyzstan Narendra Modi Rasha

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi

Gwamnatin Amurka ƙarƙashin Donald Trump ta sake sanya Najeriya cikin jerin “Ƙasashe Masu Matsala ta Musamman” saboda zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Wannan zargi ya biyo bayan jawabin da Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya yi a taron Majalisar Ɗinkin Duniya a kwanan baya.

Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP

A lokacin taron Shettima ya bayyana halin da ake ciki a Gaza a matsayin abin tausayawa, inda ya hi kira da a tabbatar da zaman lafiya ta hanyar kafa ƙasashe biyu masu zaman kansu.

Bayan jawabin nasa, wasu ƙungiyoyi suka fara yaɗa labarin cewa ana yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Najeriya, duk da cewa mutane da dama sun ƙaryata jita-jitar.

A ranar Juma’a, Trump ya wallafa wani rubutu a shafinsa na X, cewa Kiristoci na fuskantar barazana a Najeriya.

Ya yi iƙirarin cewar masu tsattsauran ra’ayi suna yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya .

Ya umarci ɗan Majalisar Amurka, Riley Moore da shugaban kwamitin kasafin kuɗi na Majalisar, Tom Cole, su binciki lamarin, sannan su gabatar masa da rahoto.

Shugaban ya ƙara da cewa ƙasarsa ba za ta zuba ido yayin da irin wannan “ta’addanci” ke faruwa a Najeriya da sauran ƙasashe ba.

Ya lashi takobin cewar Amurka za ta ci gaba da kare Kiristoci a duniya baki ɗaya.

Bayan wannan furuci, wasu sun zargi Trump da amfani da matsalar tsaron Najeriya don samun goyon bayan siyasa.

Har yanzu Gwamnatin Najeriya ba ta yi martani a kan lamarin ba, amma jami’an gwamnati a baya sun bayyana cewa rikice-rikicen da ake fama da su a ƙasar suna da nasaba da ayyukan ta’addanci, fashi, da rikicin ƙabilanci, ba addini ba.

Kalmar “Ƙasa Mai Matsala Ta Musamman” na nufin ƙasashen da Amurka ke ganin suna take haƙƙin ’yancin addini, kuma hakan na iya sa wa ta ƙaƙaba wa Najeriya takunkumai.

Idan ba a manta Najeriya ta fara shiga jerin irin waɗanda ƙasashe tun a shekarar 2020.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai