Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41
Published: 30th, August 2025 GMT
Bisa wani rahoton da jaridar Daily Trust ta wallafa, hakan ya nuna cewa, wannan shi ne karo na farko da Asusun Anita na Nijeriya ya samu karuwa tun daga watan Disambar shekarar 2021.
Kazalika, rahoton ya sanar da cewa, a watan Agusta Asusun ya ci gaba da karuwa wanda daga watan aka samu kimanin dala biliyan 1.
Wannan ya nuna yadda karuwar Asusun ta kai zuwa kaso 3.69 a kasa da makwanni uku, da suka gabata.
Bugu da karu, Asusun ya samu wannan karuwar ce, saboda yawan shigowar kudaden musaya na waje cikin kasar da kuma karin da aka samu, a bangren danyen Mai.
A cewar wasu alkaluma da Babban Bankin Nijeriya CBN ya fitar, sun bayyana cewa, a Ragnar data ga watan Agustan shekarar 2025, kudaden da ke a cikin Asusun, sun kai yawan dala biliyan 39.3 wadanda kuma a ranar 6 ga watan Agustan suka kai yawan dala biliyan 40.2 kafin kaiwarsu, zuwa wannan a dad in na yanzu.
Wasu masu yin fashin baki kan tattalin arziki, sun danganta samun wannan karin kan sauye-sauyen da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da yi ne, a fannin tattalin arzikin kasar.
Babban sashen da ya fi amfana shi ne, bangaren Asusun Ajiyar kudade na kasar da ke a kasar waje wanda ya kai yawan dala biliyan 40 kusan za a iya cewa, a cikin mako biyu, kafin Asusun ya wannan yawan a dad in na yanzu.
Karin da aka samu na Asusun Ajiya na kasar da ke a ketare, ya buna cewa, ya kai dala biliyan 39.3 a ranar daya ga watan Agusta wanda kuma a ranar Takwas ga watan Agusta, ya kai dala biliyan 39.5 inda kuma a ranar shida ga watan Agusta ya kai dala biliyan 40.2 sai kuma a ranar sha daya ga watan Agusta ya kai dala biliyan 40.65 kafin kuma ya karu zuwa dala biliyan 40.72 a ranar sha uku ga watan Agusta.
Idan za a iya tunawa, Asusun ya fara ne da kafar dama a ranar 31 ga watan Disambar shekarar 2024, inda kudaden Asusun suka kai dala biliyan 40.88.
Daga watan Janairu zuwa na Yuni, Assusun ya ragu dala biliyan 37 zuwa dala biliyan 39.
Alalmisali, Asusun na kasar wajen na kasar a farkon watan Yuli ya kasance ya tsaya kan dala biliyan 37.28 kafin ya kara karuwa zuwa matakin da yake na yanzu.
Karin karuwar Asusun ta kai ta zama da dala biliyan uku wanda hakan ya nuna cewa, ta kai ta kimanin kaso takwas a cikin watan.
Bugu da kari, wannan karuwar da Asusun Ajiya na waje na kasar ya samu wands a yanzu ya kai dala biliyan 41 tun bayan wanda kasar ta samu a shekarar 2021.
Wannan karuwar ta Asusun ta kuma nuna cewa, ta hairs wadda aka samu a shekarar 2022 zuwa shekarar 2023, wadda ta kai ta dala biliyan 38.
Bugu da karu, baya ga karuwar Asusun Ajiya na kasar waje, ita Naira ta kara samun daraja inda kuma hauhawan farashin kaya a kasar ya ragu wanda a watan Yuli ya kai kaso 21.88.
Wasu alkaluma da Hukumar Kula da Kiddiga ta kasa NBS ta fitar, sun nuna cewa, a watan Yuli an samu raguwa, idan aka kwatanta da kaso 22.22 da aka samu a watan Yuni.
Hakazalika, wani rahoton baya bayan nan, da Hukumar Kula da Farashin Kaya ta fitar sun nuna cewa, a watan Yuli sun kai kaso 0.34, wanda hakan ya nuna cewa, sun kai kasa da kaso 11.52 a watan Yuni kuma kasa da kaso 33.40 da aka samu a watan Yuli.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: ya kai dala biliyan ga watan Agusta dala biliyan 39 dala biliyan 40 a watan Agusta Asusun Ajiya kuma a ranar a watan Yuli
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya
Fadar Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa nan da wasu kwanaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai gana da takwaransa na Amurka, Donald Trump, domin tattaunawa kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya.
Mai ba wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, ne ya tabbatar da hakan a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.
Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin SudanA cewar Daniel Bwala, shugabannin biyu — Tinubu da Trump — sun yi tarayya da juna kan fahimta ta haɗin kai wajen yaƙi da ta’addanci da duk wata barazana ga bil’adama.
“A bayan nan Shugaba Trump ya taimaka wajen ba da izinin sayar wa Nijeriya makamai, kuma Shugaba Tinubu ya yi amfani da damar yadda ya kamata wajen yaƙi da ta’addanci, kuma muna da sakamakon da za mu iya nunawa,” in ji Bwala.
Ya ƙara da cewa duk wani saɓanin fahimta kan ko ‘yan ta’adda a Nijeriya na kai hari ne ga Kiristoci kaɗai ko kuma mabiyan addinai daban-daban, “za a tattauna kuma a warware su” a yayin ganawar shugabannin biyu, wadda za ta gudana “ko dai a Fadar Shugaban Kasa ta Abuja, ko a Fadar White House da ke Washington.”
Sanarwar ta zo ne bayan barazanar Shugaba Trump ta kai farmaki a Nijeriya, inda ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta fara tsara yadda za a kai hari kan ƙasar, saboda abin da ya kira “kisan gillar da ake yi wa Kiristoci” a Nijeriya.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, Trump ya ce Amurka “a shirye take ta turo sojojinta da manyan makamai zuwa Nijeriya don kare Kiristoci,” yana mai cewa idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma “mai yiwuwa ta shiga ƙasar don kawar da ‘yan ta’adda masu zafin kishin Musulunci.”
Barazanar Trump ta jawo cece-kuce bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya, ba tare da ya bayyana takamaiman inda ya samo waɗannan alƙaluman ba.
Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Tinubu ya jaddada cewa Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai kiyaye dimokuraɗiyya, wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.