Kasar Sin ta gabatar da ‘yancin samun ci gaba a matsayin hakkin dan Adam mafi muhimmanci. Ta hanyar dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka (FOCAC), ta zuba jari mai yawa a fannin samar da ababen more rayuwa, da cinikayya, da fasahohi a fadin nahiyar Afirka. Ayyuka irin su hanyar dogo na Addis Ababa zuwa Djibouti, manyan tituna, tashoshin ruwa da wutar lantarki, gadojin kan hanyar ruwa da masana’antu, duk wadannan an tanade su ne don su zama hanyar rage talauci da tallafawa al’umma.

Ta hanyar inganta yanayin rayuwa da samar da damarmakin tattalin arziki, kasar Sin ta yi nuni da cewa, tana kara karfafa martabar jama’ar Afirka ta hanyar samar musu da ci gaba.

 

’Yancin Cin Gashin kai da Kiyaye Mutuncin Kasa

Wani muhimmin jigo na diflomasiyyar kare hakkin dan Adam ta kasar Sin, ita ce samar da ka’idar ikon mallakar kasa da rashin tsoma baki kan harkokin gudanar da mulkin kasashen abokan huldarsu. Ba kamar yadda kasashen yammacin Turai ke yi ba, kasar Sin ba ta jingina sharuddan siyasa kan lamuni ko tallafin da take bayarwa, kamar sauye-sauyen shugabanci ko tsoma baki kan harkokin siyasar kasashen. Wannan tsari na Sin ya yi matukar janyo ra’ayoyin gwamnatocin kasashen Afirka, wadanda galibi ke kallon taimakon da sai an gindaya musu sharudda a matsayin tauye musu hakkin ‘yancin cin gashin kansu. Don haka kasar Sin ta gabatar da kanta a matsayin abokiyar huldar da ke daukar kasashen Afirka a matsayin kasashe masu ‘yanci ba Bayi ba.

 

Kare Rayuwa da Lafiya

Kasar Sin ta tallafawa kasashen Afirka a fannin kiwon lafiya da taimakon jin kai. Tun daga shekarar 1963 kasar Sin ta fara turo tawagar likitocinta zuwa Afirka don aikin agaji. A lokacin da cutar annobar Ebola da annobar COVID-19 ta barke a kasashen Afirka, kasar Sin ta jaddada ‘yancin rayuwa da lafiya a matsayin babban hakkin dan Adam. Irin yadda ta samar da alluran rigakafi, asibitoci, da kayan aikin likitanci, hakan ya nuna yadda kasar ke kare mutuncin dan Adam ta hanyar kare bukatunsa na halittarsa na yau da kullum.

 

Musanyar Al’adu da Mutuncin Dan Adam

Baya ga samar da tattalin arziki da kiwon lafiya, kasar Sin na ingiza yin mu’amala tsakanin jama’arta da na Afrika don karfafa mutunci da daidaito. Ba da tallafin karatu ga daliban Afirka a jami’o’in kasar Sin, shirye-shiryen al’adu, da hadin gwiwar kafofin watsa labarai, duk hakan na nufin sauya tunanin yadda kasashen yamma suka dauki Afirka. Ta hanyar karfafa mutunta al’adu da hadin gwiwa, kasar Sin ta gabatar da kanta a matsayin mai daukaka darajar mutum da kasa baki daya.

 

Kalubale da Suka

Hausawa na cewa, “sara da sassaka, ba ya hana Gamji toho”, duk wanda ya kudiri aniyar tsamo wani daga cikin kangin talauci da koma baya da wani ya jefa shi, dole sai ya fuskanci “kalubale da suka” daga wannan mai zaluncin. An ce lamunin kasar Sin ga Afirka kuma babu “tsangwama”, na nufin mallake yankin ne. Wasu kuma sun ce, matsalolin muhallin Afirka na da nasaba da ayyukan da kamfanonin kasar Sin ke yi a yankin. Duk da wannan suka, shugabannin Afirka sun jaddada kuma kullum a shirye suke kan ci gaba da kare muradun Sin domin ta tsamo su daga babakeren kasashen yammacin Turai da suka mayar da su Bayi, suna masu jaddada cewa, ci gaban da kasar Sin ke samar wa yankin, shi ne asalin kare hakkin dan Adam.

 

Da wadannan muhimman abubuwan da kasar Sin ke yi a Afirka bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”, za mu tabbatar da cewa, huldar Sin da Afirka wacce ta rataya a kan samar da ci gaba, kare ‘yancin cin gashin kai, kare mutunci, su ne hakikanin kare mutuncin dan Adam sabanin yadda kasashen yammacin Turai suka kakabawa Afirka, wai ‘yancin dan Adam, ‘yancin siyasa.

Ta hanyar ba da fifiko ga bunkasuwar tattalin arziki, da mutunta ‘yancin kai, kasar Sin ta sake fayyace ka’idojin hadin gwiwar ‘yancin dan Adam da kasashen Afirka. Ba tare da wani kalubale ba, wannan hangen nesa na kasar Sin ya yi tasiri ga yawancin ƙasashen Afirka da ke neman mutunci, daidaito, da cin gashin kai a dangantakarsu ta ƙasa da ƙasa.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Sin ta

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

A cewarsa, ta hanyar wadannan shirye-shirye, kasar Sin ta nuna goyon baya mai dorewa ga kasashe masu tasowa kuma tana ba da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban duniya a karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher