Mutane Da Dama Sun Tsere Sakamakon Harin ‘Yan Bindiga A Neja Da Kwara
Published: 29th, August 2025 GMT
Da aka tuntubi Kwamishinan Tsaron Cikin Gida, Birgediya Janar Bello Abdullahi Mohammed mai ritaya, ya tabbatar da faruwar al’amarin, amma ya ce; jami’an tsaro sun shawo kan lamarin.
Haka zalika, mazauna Ndanaku da ke Karamar Hukumar Patigi a Jihar Kwara, sun kauracewa wurin sakamakon hare-haren ‘yan bindiga.
Kwamandan ‘yan banga, Gina Gana; wanda shi ma yana daya daga cikin wadanda suka tabbatar da faruwar lamarin, ya bayyana cewa; an kai hare-hare guda biyu ne kwanaki uku da suka gabata, wanda ya tayar wa da kowa hankali a garin.
Har wa yau, a makon day a gabata ne Gwamna AbdulRahman AbdulRazak, ya yi taro da wasu masu ruwa da tsaki na Ifelodun, inda ya yi bayani dalla-dalla kan kokarin da suke yi na magance matsalar rashin tsaro. Da yake magana a kan hadin gwiwa da ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro da sauran dukkanin hukumomin tsaro, gwamnan ya bayyana cewa; ana yin dukkanin abin da ya kamata, domin kawar da duk wata barazana ta tsaro a jihar, ciki har da Ifelodun, Patigi da Edu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp