An gudanar da bikin cika shekaru 30 da kafuwar asusun hadin gwiwar kasashe masu tasowa na MDD a birnin New York, babban birnin Amurka.

Yayin bikin, zaunannen wakilin Sin dake MDD, Fu Cong, ya fitar da jawabi cewa, bangaren Sin ya yaba da sakamakon hadin gwiwa mai inganci da asusun ke goyon baya. Kuma Sin za ta ci gaba tsayawa tsayin daka kan goyon bayan ginshikin ci gaban MDD, da goyon bayan ra’ayin bangarori daban daban na gaskiya da kuma daukar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashe masu tasowa a matsayin abin dake kan gaba a cikin hadin gwiwar da Sin ke yi da kasashen waje.

An kafa asusun hadin gwiwar kasashe masu tasowa a shekarar 1995, wanda ofishin kula da hadin gwiwar kasashe masu tasowa na MDD ke gudanarwa, da nufin habaka ci gaba mai dorewa da kawo sauyin fasaha ta hanyar hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa da kuma taimaka wa kasashen su iya magance kalubalen ci gaba tare.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasashe masu tasowa hadin gwiwar

এছাড়াও পড়ুন:

Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran

Mai ba da shawara ga jagoran juyin juya halin Musulunci ya mayar da martani ga barazanar shugaban kasar Amurka kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran

Ali Shamkhani mashawarcin Jagoran juyin juya halin Musulunci a fagen siyasa ya jaddada cewa: Iran kasa ce mai cin gashin kanta mai tsayayyen tsarin tsaro, al’umma masu tsayin daka, da jajayen layi. Ya jaddada cewa, “tattaunawa hanya ce ta ci gaba da kuma kiyaye moriyar kasa da mutunci, ba kayan aiki na tilastawa ko mika wuya ba.”

Shamkhani ya rubuta a shafinsa na dandalin X cewa: “Burin isa ga cibiyoyin nukiliyar Iran da kuma ‘tarwatsa su’ ba komai ba ne illa mafarki da shugabannin Amurka da suka gabata sun kasance sun yi has ashen hakan.

Ya kara da cewa: Iran kasa ce mai cin gashin kanta, mai tsarin tsaro mai karfi, mutane masu juriya da jajayen layi. Ya kuma jaddada cewa tattaunawa ita ce hanyar samun ci gaba da kuma kiyaye moriyar kasa da mutunci, ba tilastawa ko mika wuya ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Gargadi Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Da Wasu Kasashe
  • Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
  • Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
  • Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba 
  • Save The Children Ta Shirya Taron Bita Ga Yan Jarida Da Kungiyoyi Masu Zaman Kansu A Kaduna.
  • Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba
  • Yemen: Matukar Gaza Tana Fuskantar Yaki, To Babu Tsaro A HKI
  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran