Aminiya:
2025-05-21@22:55:04 GMT

Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano

Published: 21st, May 2025 GMT

Ƙungiyar ma’aikatan wutar lantarki ta Najeriya (NUEE) reshen Jihar Kano, ta tsunduma yajin aikin sai baba-ta-gani saboda rashin biyan haƙƙoƙinsu da kamfanin KEDCO ke yi.

Sakataren tsare-tsaren ƙungiyar na shiyyar Arewa maso Yamma, Muhammad Babangida ne, ya bayyana hakan a wani saƙon murya da Freedom Radio ta wallafa.

Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”

A cewarsa, ma’aikatan KEDCO sun shafe sama da watanni 100 ana cire musu kuɗin fansho daga albashinsu, amma ba a tura kuɗin zuwa inda ya dace ba.

“Tun bayan kafa KEDCO aka fara cire wa ma’aikata kuɗin fansho, amma har zuwa yanzu ba a tura su inda ya kamata.

“Waɗanda suka mutu ko suka bar aiki suna cikin wannan hali, ba a biya su haƙƙinsu ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa duk wani ƙoƙarin da suka yi don sulhu da kamfanin ya ci tura, hakan ya sa suka yanke shawarar shiga yajin aiki.

Ya ce: “Kamfanin KEDCO yana samun kuɗi sosai, amma ya gaza biyan haƙƙin ma’aikata.

“Saboda haka, daga idan mutane sun ga an samu katsewar wuta, ka da su ɗora laifi a kanmu.”

Yajin aikin zai shafi harkokin samar da wutar lantarki a Kano da kewaye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Wutar Lantarki Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Queen Zeeshaq za ta shiga daga ciki

Zainab Ishaq Muhammad, wadda aka fi sani da ‘Queen Zeeshaq’ za ta shiga daga ciki a ranar Lahadi mai zuwa.

Duk da cewa ba a yayata batun auren ba, Aminiya ta tabbatar da ganin katin gayyata da ke nuna za a ɗaura auren nata da angonta, Hussain Muhammad Koya, a ranar 25 ga watan Mayu, 2025.

’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato

Rahotanni sun nuna cewar a ranar Laraba za a fara bidirin bikin har zuwa ranar Asabar.

An shirya gudanar da walima, ƙwallon ƙafa, saukar karatun Alƙur’ani da sauransu har zuwa ranar ɗaurin aure.

A yanzu matashiyar ta fi mayar da hankali wajen ayyukan jin-ƙan marayu da kuma aikin jarida.

Aminiya ta tuntuɓi makusantan mawaƙiyar don jin dalilin ɓoye bikin, amma sun ce wasu dalilai ne ya sa suka ɗauki wannan mataki.

Matashiyar ta fice a kafafen sada zumunta musamman Facebook, inda ake yin gwagwarmaya da ita kan harkokin yau da kullum.

Ga katin bikin a ƙasa:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC
  • Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo
  • Queen Zeeshaq za ta shiga daga ciki
  • Malamai sun gindaya sharaɗi kafin janye yajin aiki a Abuja 
  • ’Yan bindiga: Zamfara sun koma kwana a jeji
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22
  • Uwargidar Gwamnan Zamfara Ta Sake Jaddada Kudurin Dakile Tu’ammali Da Miyagun Kwayoyi A Jihar
  • An cimma matsaya kan dakatar da haska fina-finai 22 a Kano
  • HKI Ta Bude Kofofin Shigar Kayakin Agaji Zuwa Cikin Gaza A Karon Farko Bayan Kimani Watanni 2.5