Amurka ta sake kai Hari a yankunan Saada da Hudaidah na Yemen
Published: 1st, May 2025 GMT
Jiragen yakin Amurka sun sake kai hare-hare da dama kan lardunan Saada da Hudaidah na kasar Yemen yau Alhamis.
Wata majiyar tsaro a Yemen ta kara da cewa, an kai wasu hare-hare uku a yankin Kataf da ke lardin Saada, yayin da wani kuma ya afkawa gundumar al-Houk da ke lardin Hudaidah a gabar tekun yammacin Yeman, lamarin da ya janyo hasarar kayayyaki na fararen hula.
Dama a cewar kafar yada labaran kasar Yemen Al-Masirah, jiragen yakin Amurka sun kai hari a gundumar al-Sayl da ke lardin al-Jawf a arewacin kasar Yemen ranar Laraba.
Tun a ranar 15 ga watan Maris da ya gabata ne, kawencen Amurka da Birtaniya ke kai hare-hare ta sama kan kasar Yamen, domin nuna goyon baya ga gwamnatin Isra’ila.
Kafin hakan a ranar Litinin, 28 ga watan Afrilu, Amurka ta kai wani mummunan hari ta sama a birnin Sanaa, inda ta kashe mutane akalla 12 tare da jikkata wasu hudu.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta kasar Yemen ta fitar ta ce an kashe ‘yan kasar Yemen 12 da suka hada da kananan yara, yayin da wasu hudu suka jikkata sakamakon harin da Amurka ta kai kan wasu gidajen zama a yankin Thaqban na birnin Sanaa.
A safiyar litinin jiragen yakin Amurka sun kai harin bam a daya daga cikin wuraren da ake tsare da bakin haure ‘yan Afirka da ke yankin Saada, inda suka kashe mutane 68 tare da jikkata 47.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
Miliyoyin Iranauawa Sun Fito Makokin 8 Ga Watan Muharram
Miliyoyin Iraniyawa a ranar 8 ga watan muharram sun fito sanye da bakaken kaya da tunawa a bubuwan da suka faru a ranar kwanakin Asoora inda aka kashe Imam Hussain (a) jikan manzon All… Banda wannan raya kwanakin Ashoora ci gaba ne da nuna turjiya da kuma saukar da kai kan azzaluman shuwagabanni ko da ba tare da samun nasara a zahiri ba kuma nan kusa ba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa an gudanar da taturrukan Ashoora a duk fadin Iran, kuma a yau Tasoo’a za’a ci gaba da fitowa har zuwa gobe a Ashoora randa Imam Hussain (a) tare da sahabbansa 72 suka yi shahada a hannun sojojin yazeed a Karbala a ranar 10 ga watan Muharram shekara ta 61 H.K..
A wannan karon ranakun Ashoora sun zo ne a dai-dai lokacinda aka kammala yakin 12 da HKI da Amurka, kuma ginin sojojin Iran sun sami nasara a kan HKI a yankin, wannan ya hada kan mutanen kasar Iran a irin wannan kwanakin don raya wadan nan kwanaki wadanda ake daukasu a matsayin kanaki masu karfafa guiwan sojoji da mutanen kasar wajen yaki da makiya da kuma samun nasara a kansu.
Muna mika ta’aziyyar mu ga dukkan musulmi da kuma masu nemen yenci a duniya da zagayowar kwanakin juyayen Asoorah.