An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna
Published: 20th, April 2025 GMT
Kungiyar Masu Babura Uku ta Najeriya, Jihar Kaduna ta Rantsar da Shugabannin Sassa Goma Sha Biyar da Manyan Jami’ansu don Gudanar da Harkokin Kungiyar a Tsawon Shekaru Hudu Masu Zuwa.
Mataimakin Kwamandan Hanya kuma Mataimakin Jami’in Wayar da Kai na Hukumar Kiyaye Haddura ta Tarayya (FRSC), Kaduna, Usman Garba, wanda ya yi magana da manema labarai bayan bikin rantsarwa, ya yaba wa kungiyar, yana mai cewa wannan ci gaba ne mai kyau ga kungiyar.
Ya ce Hukumar Kiyaye Haddura na farin ciki da wannan ci gaba saboda sabon tsarin shugabanci zai taimaka wajen magance matsalolin da suka shafi direbobin babura uku (Keke Napep) da hukumar ke fuskanta a jihar.
A cewarsa, yanzu hukumar za ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar wajen horas da mambobinta kan amfani da hanyoyin mota da kuma basu ilimi na musamman lokaci zuwa lokaci domin su san yadda za su yi amfani da hanyoyin jama’a yadda ya kamata.
A nasa jawabin, Shugaban Kungiyar Masu Babura Uku ta Najeriya, Jihar Kaduna, Kwamared Jacob Ayuka, ya bayyana cewa kungiyar na taka muhimmiyar rawa a harkar sufuri ta Najeriya.
Ya bayyana cewa, tare da karfi a matakin tushe da kuma samun karbuwa a kasa baki daya, kungiyar na ci gaba da fafutukar ganin an samu ingantattun dokoki, da karfafa wa mambobinta gwiwa, tare da bada gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya.
Kwamared Ayuka ya kara da cewa kungiyar na aiki a matsayin kungiya mai tsari, ba mai neman riba ba, wacce ke kokarin tallafa wa mambobinta ta hanyar fafutuka, shirye-shiryen jin kai, tallafin aiki, da kuma hadin gwiwa da hukumomin gwamnati da hukumomin sufuri.
An rantsar da shugabannin sassa goma sha biyar da jami’ansu bayan gudanar da zabe, kuma an mikawa kowane shugaban sashi takardar shaida ta nasara.
Daga cikin shugabannin da aka rantsar akwai:
Sashin Wusili – Kwamared James Ibrahim Yakubu;
Unguwan Mu’azu – Kwamared Mustapha Aliyu;
Urban Shelter – Kwamared Shehu Lawal;
Kasuwar Sabo – Kwamared Emmanuel Okiki John;
Rain Oil – Kwamared Jacob Ayuka.
Sauran su ne:
Tashar ‘Yan sanda Tsohuwar – Kwamared Paul Dogo;
Rukunin Narayi Junction – Kwamared Tanimu Mohammed;
Jami’ar KASU – Kwamared Sani Adam;
Kongo, Zaria – Aminu Ibrahima.
Kana kuma:
Jan-Ruwa – Kwamared Patrick A. Sanda;
Hayin Mal Bello – Kwamared Abubakar Ilyasu;
FCE Zaria – Kwamared Isyaka Baba Tanko;
Charity – Kwamared Jatau Ango Manga;
Bakin-Ruwa – Kwamared Mahadi Lawan;
AP Maraban Rido – Kwamared Livinus Solomon.
Mataimakin Kwamandan Hanya kuma Mataimakin Jami’in Wayar da Kai na FRSC Kaduna, Usman Garba, na mika takardar shaida ga daya daga cikin shugabannin sassan a yayin bikin.
A nasa bangaren, shugaban sashin Kasuwar Sabo, Kwamared Emmanuel Okiki John, ya bayyana cewa sashin kasuwa ne mai cike da aiki, wanda ke da korafe-korafe da dama, kuma akwai shirin da aka tanadar don gyara lamura.
Kwamared John ya sha alwashin yin aiki tukuru tare da sauran shugabanni don amfanin da ci gaban mambobin kungiyar.
Cov/ Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da jijjiga sakamakon sauya sheƙar da ’yan siyasa daga ɓangarori daban-daban suke yi.
A baya-bayan nan tsallakawar da wasu jiga-jigan jam’iyyun adawa suka yi zuwa Jam’iyyar APC mai mulki ta jawo ɗiga ayar tambaya a kan dalilansu da kuma makomar hamayya a zaɓen 2027.
Hakan dai yana faruwa ne a daidai lokacin da wasu ’yan ƙasar suke kokawa bisa yadda ake gudanar da mulki da kuma yadda wasu manyan ’yan siyasa suke fadi-tashin kafa wata inuwa da suka ce za ta ciro wa talaka kitse a wuta ta hanyar kawar da gwamnatin APC.
NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin ArewaWannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai da nufin gano alƙiblar da siyasar Najeriya take shirin fuskanta.
Domin sauke shirin. Latsa nan