Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@00:07:33 GMT

An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna

Published: 20th, April 2025 GMT

An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna

 

Kungiyar Masu Babura Uku ta Najeriya, Jihar Kaduna ta Rantsar da Shugabannin Sassa Goma Sha Biyar da Manyan Jami’ansu don Gudanar da Harkokin Kungiyar a Tsawon Shekaru Hudu Masu Zuwa.

 

Mataimakin Kwamandan Hanya kuma Mataimakin Jami’in Wayar da Kai na Hukumar Kiyaye Haddura ta Tarayya (FRSC), Kaduna, Usman Garba, wanda ya yi magana da manema labarai bayan bikin rantsarwa, ya yaba wa kungiyar, yana mai cewa wannan ci gaba ne mai kyau ga kungiyar.

 

Ya ce Hukumar Kiyaye Haddura na farin ciki da wannan ci gaba saboda sabon tsarin shugabanci zai taimaka wajen magance matsalolin da suka shafi direbobin babura uku (Keke Napep) da hukumar ke fuskanta a jihar.

 

A cewarsa, yanzu hukumar za ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar wajen horas da mambobinta kan amfani da hanyoyin mota da kuma basu ilimi na musamman lokaci zuwa lokaci domin su san yadda za su yi amfani da hanyoyin jama’a yadda ya kamata.

 

A nasa jawabin, Shugaban Kungiyar Masu Babura Uku ta Najeriya, Jihar Kaduna, Kwamared Jacob Ayuka, ya bayyana cewa kungiyar na taka muhimmiyar rawa a harkar sufuri ta Najeriya.

 

Ya bayyana cewa, tare da karfi a matakin tushe da kuma samun karbuwa a kasa baki daya, kungiyar na ci gaba da fafutukar ganin an samu ingantattun dokoki, da karfafa wa mambobinta gwiwa, tare da bada gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya.

 

Kwamared Ayuka ya kara da cewa kungiyar na aiki a matsayin kungiya mai tsari, ba mai neman riba ba, wacce ke kokarin tallafa wa mambobinta ta hanyar fafutuka, shirye-shiryen jin kai, tallafin aiki, da kuma hadin gwiwa da hukumomin gwamnati da hukumomin sufuri.

 

An rantsar da shugabannin sassa goma sha biyar da jami’ansu bayan gudanar da zabe, kuma an mikawa kowane shugaban sashi takardar shaida ta nasara.

 

Daga cikin shugabannin da aka rantsar akwai:

 

Sashin Wusili – Kwamared James Ibrahim Yakubu;

 

Unguwan Mu’azu – Kwamared Mustapha Aliyu;

 

Urban Shelter – Kwamared Shehu Lawal;

 

Kasuwar Sabo – Kwamared Emmanuel Okiki John;

 

Rain Oil – Kwamared Jacob Ayuka.

 

Sauran su ne:

 

Tashar ‘Yan sanda Tsohuwar – Kwamared Paul Dogo;

 

Rukunin Narayi Junction – Kwamared Tanimu Mohammed;

 

Jami’ar KASU – Kwamared Sani Adam;

 

Kongo, Zaria – Aminu Ibrahima.

 

Kana kuma:

 

Jan-Ruwa – Kwamared Patrick A. Sanda;

 

Hayin Mal Bello – Kwamared Abubakar Ilyasu;

 

FCE Zaria – Kwamared Isyaka Baba Tanko;

 

Charity – Kwamared Jatau Ango Manga;

 

Bakin-Ruwa – Kwamared Mahadi Lawan;

 

AP Maraban Rido – Kwamared Livinus Solomon.

 

Mataimakin Kwamandan Hanya kuma Mataimakin Jami’in Wayar da Kai na FRSC Kaduna, Usman Garba, na mika takardar shaida ga daya daga cikin shugabannin sassan a yayin bikin.

 

A nasa bangaren, shugaban sashin Kasuwar Sabo, Kwamared Emmanuel Okiki John, ya bayyana cewa sashin kasuwa ne mai cike da aiki, wanda ke da korafe-korafe da dama, kuma akwai shirin da aka tanadar don gyara lamura.

 

Kwamared John ya sha alwashin yin aiki tukuru tare da sauran shugabanni don amfanin da ci gaban mambobin kungiyar.

 

Cov/ Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kungiyar Rantsarda

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

Wani mummunan hatsarin mota a hanyar Kaduna zuwa Zariya ya yi sanadin mutuwar mutum takwas ’yan gida daya, yayin da wasu mutum biyu ke can kwance a asibiti rai a hannun Allah.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne wajen misalin karfe 6:00 na yammacin ranar Litinin a garin Barakallahu da ke kan hanyar Kaduna zuwa Zariya, ana tsaka da bukukuwan Babbar Sallah.

A cewar rahotannin, lamarin ya faru ne lokacin da wata mota da ke tsala gudu ta kwace sannan ta danne mutanen da ke tsaye a gefen hanya bayan dawowarsu daga yawon sallah.

Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India

A cewar mahaifin mamatan, Malam Jamilu Usman Maiyadi, wata mota kirar GLK Marsandi mai ruwan toka ce ta take iyalan nasa, kuma wani yaro ne yake tuka ta.

Sai da a cewarsa, yaron wanda suka yi ittifakin dan gidan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin, ya cika wandonsa da iska bayan faruwar lamarin.

Ya ce, “Mun rasa iyalai takwas ’yan gida daya a rana daya. Daga ciki akwai matata Khadija Umar da ’ya’yana su biyu sai kuma kanne da yayyen matar tawa da kuma wata gwaggonsu, duk sun mutu.

“A jimlance, mutum takwas kenan motar ta take; takwas sun mutu nan take, biyu kuma har yanzu suna asibiti,” in ji shi.

Malam Jamilu ya ce iyalan nasa na tsaye ne a bakin hanya suna jiran su sami motar da za ta kai su gida lokacin da motar ta kwace daga kan titi ta afka musu.

Ya kuma ce, “Tabbas motar na gudun wuce sa’a lokacin faruwar lamarin saboda kafar matata ta yi karayar da ba za a iya gyarawa ba, sannan sai jami’an hukumar kiyaye hadura ne ma daga baya suka gano wasu sassan jikin dana Sadiq,” Malam Jamilu ya fada fuskarsa cike da alhini.

‘Har da mai cikin wata takwas da za ta haifi tagwaye a cikin wadanda suka mutu’

Daga cikin wadanda suka rasu har da Zainab Muhammad wacce ke dauke da juna-biyun wata takwas da za ta haifi tagwaye.

Mijin marigayiyar, Sulaiman Abdulkadir Mai Shinkafa, wanda malamin addini ne a Hayin Rigasa, ya bayyana lamarin a cikin alhini.

Ya ce, “Ta kusa haihuwa. Mun riga mun sayi duk kayan jarirai muna shirye-shiryen haihuwar. Har mun ma sanya wa jariran sunan Hassan da Hussaini. Sannan akwai danmu mai shekara shida mai suna Khalid da aka kashe.

“An take matar tawa, sannan dana sai da muka kankaro namansa da katako kafin a yi musu jana’iza. Abu ne da babu wanda zai yi fatan ya gani a rayuwarsa.”

‘Ko uffan iyalan yaron da ya take mu ba su ce mana ba’

Kamar sauran masu alhinin, Malam Sulaiman ya nuna takaici kan yadda ya ce iyalan yaron da gwamnati sun yi watsi da su ko uffan ba su ce musu ba.

“Babu wani daga cikin iyalan yaron, wanda dan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin da ya tuka motar, ko kuma daga gwamnatin jihar Kaduna da ya zo ya yi mana ta’aziyya.

“Ko uffan ba su ce mana ba. hatta mahaifin direban motar bai zo ba, sai ka ce yaruwar iyalan namu ba ta da wani amfani,” in ji shi.

Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) ta tabbatar da faruwar lamarin inda ta alakanta shi da gudun wuce sa’a da kuma kwacewar mota a kan hanyar da ba a jima da dauke ruwan sama ba.

Kwamandan shiyya na hukumar a Kaduna, Tijjani Iliyasu ne ya tabbatar da hakan.

Sai dai ya ce sun mika lamarin zuwa hannun ’yan sanda domin fadada bincike a kai.

Kazalika, duk kokarin wakilinmu na jin ta bakin rundunar ’yan sandan Kaduna da gwamnatin jihar sun ci tura saboda sun ki cewa komai a kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki